Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiKu dakatar da zanga-zangar adawa da Gwamnatin Tinubu - APC ta gargadi...

Ku dakatar da zanga-zangar adawa da Gwamnatin Tinubu – APC ta gargadi ‘yan Nijeriya

Jam’iyyar APC shiyyar Arewa ta tsakiya ta gargadi matasa da wasu kungiyoyi da ke shirin yin zanga-zangar adawa da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Jam’iyyar ta ce irin wannan shawarar ba za ta yi tasiri ba kuma illa ce ga ci gaban kasar a halin yanzu,  tana mai kira ga masu shirya gangamin da su sake tunani tare da dawo da matasa kan hanyar dai-dai.

Shugaban Jam’iyyar, Alhaji Saleh Mandung Zazzaga, wanda ya yi wa manema labarai jawabi a ranar Litinin a Jos, babban birnin Jihar Filato, ya ce ya kamata masu kira a gudanar da zanga-zangar su lura da halin da ake ciki a kasar.



Zazzaga ya ce, shugaba Tinubu na kokarin mayar da kasar nan kan turbar ci gaba, inda ya bukaci ‘yan Nijeriya da su mara masa baya.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata