Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiKu sanya ido sosai kan zaben da za a gudanar a 2027...

Ku sanya ido sosai kan zaben da za a gudanar a 2027 – Kiran Peter Obi ga ‘yan Nijeriya

Tsohon ɗan takarar shugabacin Nijeriya Peter Obi, ya yi kira ga ’yan kasar da su kasance masu sa ido sosai a zaɓen 2027, yana jaddada cewa dole ne kowace ƙuri’a a kirga ta, tare da yin gargaɗi ga duk wanda zai yi ƙoƙarin kawo cikas ga sahihin zaɓe.

Jaridar Punch ta rawaito cewa Obi ya wallafa saƙon ne a shafinsa na X, inda ya bukaci masu jefa ƙuri’a su tsaya a rumfunan zaɓe bayan sun kaɗa ƙuri’unsu domin su shaida an ƙirga da kuma tura sakamakon zuwa hukumomi.

Obi ya ce halartar jama’a da sa ido a rumfunan zaɓe na da matuƙar muhimmanci wajen kare dimokiraɗiyya da hana maguɗin zaɓe.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata