Rahoton jaridar Daily Trust ya nuna cewa kuɗin da aka bai wa ƴan wasan ƙungiyar mata ta Nijeriya Super Falcons, bayan nasararsu a gasar WAFCON 2024, ya kai adadin da zai iya biyan albashin fiye da likitoci 16,000, malamai 66,000, da kuma fiye da ‘yan sanda 78,000 da ke matakin albashi mafi ƙasa, na wata guda.
Rahoton ya jaddada cewa a lokacin da ƙasar ke fama da matsalolin rashin isasshen albashi da yin ƙaurar likitoci zuwa ƙasashen waje, wasu ma’aikatan lafiya a wasu jihohi na karɓar ƙasa da Naira 250,000 a wata, duk da cewa suna fuskantar barazana ga rayuwarsu wajen ceton jama’a.
Gwamnatin Tinubu da kungiyar gwamnonin kasar dai sun fitar da Naira biliyan 4.95 a matsayin lada ga ƴan wasa da masu horar da su, tare da bai wa kowanne gida mai ɗakuna uku a sabon shirin gidaje na “Renewed Hope Estate”.
