A wata sanarwa da kungiyar ta fitar mai dauke da sa hannun shugabanta kuma shugaban kasar Burkina Faso kyaften Ibrahim Traoré, ta yi kakkausan suka kan harin da ta danganta da na dabbanci akan kasar ta Nijar da ke memba a kungiyar.
AES ta ce wannan hari wata barazana ce ga tsaron harin gwiwa na kasashen, kwanciyar hankalin yankin da kuma kokarin da suke yi tare na kawo zaman lafiya da ci gaban yankin Sahel.
Kazalika kungiyar ta yi kakkausan suka da gargadi ga duk masu tallafawa ‘yan ta’adda da kudi, makamai, ko da bayanan sirri ko kuma goyan baya a siyasance cewa sai sun amsa alhakin abinda suka aikata.
