Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta soki gwamnatin Nijeriya kan yadda ta ci gaba da yin shiru tsawon shekara shida bayan bacewar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata, ba tare da wani bayani ko bincike mai ma’ana ba.
Dadiyata, wanda malami ne a Sashen Harsuna na Jami’ar Tarayya Dutsinma, kuma fitaccen mai sharhi a kafafen sada zumunta daga jihar Kaduna, ya bace ne tun ranar 2 ga Agusta, 2019, bayan wasu da ba a san ko su wanene ba sun tafi da shi daga gidansa da misalin ƙarfe 1 na dare.
A wani taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna ranar Asabar, Isa Sanusi, Daraktan Amnesty International a Nijeriya, ya bayyana cewa rashin jajircewar gwamnati wajen gano inda Dadiyata yake ko binciken lamarin ya kara nuna hadarin da masu sukar gwamnati ke fuskanta a kasar.
Sanusi ya kara da cewa wannan lamari yana nuni da irin halin matsin lamba da ‘yan Nijeriya ke ciki wajen bayyana ra’ayoyinsu cikin ‘yanci, yana mai kira ga gwamnati da ta dauki mataki gaggawa domin fayyace gaskiyar lamarin tare da kare hakkin dan Adam a kasar.
Kungiyar Amnesty International ta caccaki gwamnatin Nijeriya kan shiru, bayan shekara 6 da batan Dadiyata
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
