Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiKungiyar iyayen daliban Zamfara 88 da ke makale a Cyprus ta nemi...

Kungiyar iyayen daliban Zamfara 88 da ke makale a Cyprus ta nemi agajin gwamnati

Kungiyar iyayen daliban Zamfara da ke karatu a Cyprus ta roƙi Gwamnan jihar, Dauda Lawal, da ya biya bashin da ya kai fiye da Naira biliyan 1 da ake binsu, domin ɗaliban su samu damar ci gaba da karatu.

Shugaban ƙungiyar, Ibrahim Tudu, ya bayyana cewa ɗaliban sun shiga mawuyacin hali sakamakon ƙarewar kuɗin makaranta, izinin zama, da na haya, tare da fama da ƙarancin abinci.

A cewar rahoton jaridar Premium Times, Ibrahim Tudu ya musanta rahotannin da ke cewa gwamnatin jihar ta riga ta biya Naira miliyan 290, amma ɗaliban sun ƙi komawa gida duk da basu tikitin jirgi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata