Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiKungiyar Kiristoci ta CAN ta nuna rashin gamsuwa da hukumar Hisbah da...

Kungiyar Kiristoci ta CAN ta nuna rashin gamsuwa da hukumar Hisbah da aka kafa a jihar Neja

Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen jihar Neja, CAN, ta bayyana rashin gamsuwa da kudurin dokar Hisbah da majalisar dokokin jihar ke shirin amincewa da ita inda tace hakan na nuna wariya da nuna bambanci ga Kiristoci.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa CAN ta ce dokar za ta ƙara raba kan al’umma da ke addini daban-daban a jihar, maimakon ta ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai.

Shugaban CAN na jihar Neja, Most Rev. Bulus Dauwa Yohanna, ya yi gargadin cewa kudurin dokar hukumar Hisbah wanda ɗan majalisar da ke wakiltar mazabar Chanchaga, Mohammed Abubakar, ya gabatar, na iya jawo cece-kuce kuma bai kamata bangaren zartarwa ya amince da shi ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata