Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiKungiyar kwadago ta bukaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da dokokin...

Kungiyar kwadago ta bukaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da dokokin harajin da aka gurbata

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta bukaci ’yan Nijeriya da su ƙi duk wata dokar haraji da aka ce an sauya ko an yi mata magudi.

Shugaban kungiyar, Joe Ajaero, ya bayyana haka a sakon Kirsimetinsa na 2025, yana mai cewa irin waɗannan dokoki na rusa amincewar jama’a.

Ajaero ya ce ya kamata a tabbatar da adalcin haraji, inda masu hali za su biya daidai gwargwado, yana mai cewa dokar da ke ɗauke da magudi ko ƙirƙira ba za a amince da ita ba.

A halin da ake ciki, kwamitin wucin-gadi na Majalisar Wakilai da ke binciken zargin sauye-sauye a dokokin haraji ya ce zai kammala aikinsa cikin gaggawa domin miƙa rahoto ga majalisar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata