Ƙungiyar masu gidajen sayar da man fetur ta Najeriya ta nuna rashin amincewa da shirin Dangote Refinery na fara raba kayayyakin man fetur kai tsaye zuwa gidajen mai a fadin ƙasar.
A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun ƙungiyar na ƙasa, Joseph Obele, ya fitar a ranar Litinin, PETROAN ta bayyana cewa wannan tsari na iya zama barazana ga ‘yan kasuwa da ke harkar man fetur a matakin ƙasa, tare da haifar da matsin lamba ga ayyukan yi a fannin.
A rahoton da jaridar Daily Trust ta fitar, Dangote Refinery dai ta sanar da shirin faɗaɗa rabon man fetur zuwa manyan gidajen mai a fadin ƙasa a ƙarshen mako da ya gabata.
