Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiKungiyar Miyetti Allah ta yi alkawarin aiki hannu da hannu da jami’an...

Kungiyar Miyetti Allah ta yi alkawarin aiki hannu da hannu da jami’an tsaro a jihar Kaduna

Kungiyar Miyetti Allah (MACBAN) reshen Kudancin Kaduna ta bayyana aniyar haɗa kai da hukumomin tsaro domin magance matsalar tsaro a yankin.

Wannan kudiri ya fito ne a taron da aka gudanar a Kafanchan, hedkwatar karamar hukumar Jema’a, a ranar Lahadi.

Shugaban MACBAN na yankin Kudancin Kaduna, Alhaji Mato Yahaya, ya ce lokaci ya yi da za a nemo mafita, tare da yin kira ga shugabanni su faɗi gaskiya kuma su gabatar da shawarwari masu amfani domin magance matsalolin yankin. Ya kuma jaddada muhimmancin zaman lafiya tsakanin makiyaya da sauran al’umma.

A nasa jawabin, shugaban MACBAN na jihar Kaduna, Alhaji Abdulhamid Albarka, ya ce an shirya taron ne domin tattara ra’ayoyin jagororin Fulani na ƙananun hukumomi, sannan a mika su ga hukumomin tsaro domin ɗaukar matakin da ya dace.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata