Monday, April 6, 2026
HomeKetareKungiyar MPLJ a Nijar ta dau alhakin hari kan bututun man Nijar...

Kungiyar MPLJ a Nijar ta dau alhakin hari kan bututun man Nijar a yankin Agadem

Kungiyar ‘yan tawaye ta’ Mouvement Patriotique pour la Liberté et la Justice’ wato MPLJ ta dauki alhakin harin da aka kai a wannan rana ta 16 ga watan Nuwamba kan bututun man Nijar, kusa da cibiyar hakar man fetur ta Agadem da ke jihar Diffa.

Kungiyar tawayen ta sanar da daukan alhakin wannan hari ne a cikin wata sanarwar da ta fitar a wannan rana ta Lahadi mai dauke da sa hannun shugabanta Moussa Konai.

 

A cikin sanarwar, kungiyar ta ce ta kai wannan hari ne biyo bayan karewar wa’adin da ta bada a sanarwar ta ta karshe, inda ta gargadi kamfanoni da masana’antu masu hakar ma’adanai kan su guji hada kai da hukumomin Nijar wadanda ta ke adawa da su.

Kazalika kungiyar ta MPLJ ta ce muddin aka ci gaba da yin biris da gargadinta, za ta zafafa kai irin wadannan hare-hare har sai an kai ga rufe kamfanin tace mai na SORAZ sannan kuma a mayar da kasar kan turbar dimukuradiyya.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata