Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiLibya ta kora 'yan Nijeriya 80 gida saboda zama ba bisa ka'ida...

Libya ta kora ‘yan Nijeriya 80 gida saboda zama ba bisa ka’ida ba a kasar

Hukumomin Libiya sun kori ’yan Nijeriya 80 daga ƙasar bayan kama su suna zama ba bisa ƙa’ida ba, a wani yunkuri na rage cinkoso a cibiyoyin da ake tsare masu aikata irin laifin.

Hukumar yaki da masu shiga kasar ba bisa ka’ida ba tare da haɗin gwiwar ofishin jakadancin Nijeriya da ke Tripoli ne suka jagoranci mayar da su ta filin jirgin sama na Mitiga International Airport a ranar Laraba.

Kungiyar Migrant Rescue Watch, wadda ke sa ido kan walwalar ’yan ci-rani a Libiya, ta bayyana cewa an kora mutanen ne bisa umarnin kotu da hukumar ’yan sanda ta fitar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata