Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiMa'aikatan lafiya sun dakatar da yajin aiki bayan kwanaki 84

Ma’aikatan lafiya sun dakatar da yajin aiki bayan kwanaki 84

Ƙungiyar ma’aikatan lafiya ta JOHESU ta gargaɗi gwamnati da kada a gallaza ko hukunta mambobinta, bayan ta dakatar da yajin aikin ƙasa baki ɗaya na kwanaki 84.

JOHESU ta sanar da dakatar da yajin aikin ne a ƙarshen taron gaggawa na kwamitin zartarwa na Ƙasa (NEC) da ta gudanar a Abuja.

An kira taron ne domin nazarin sakamakon zaman sulhu tsakanin gwamnatin tarayya da JOHESU, wanda aka gudanar a hedikwatar ma’aikatar ƙwadago da ayyukan yi ta tarayya a ranar Alhamis.

A cikin sanarwar haɗin gwiwa da ta fitar bayan taron, ƙungiyar ta ce an dakatar da yajin aikin ne domin ba da damar aiwatar da sharuɗɗan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin gwamnatin tarayya da JOHESU.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata