Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiMajalisa dattawa ta ce ba za ta mayar da Natasha ba har...

Majalisa dattawa ta ce ba za ta mayar da Natasha ba har sai ta karɓi takardar hukuncin kotu

Majalisar Dattijai ta Nijeriya ta bayyana cewa ba za ta mayar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ba har sai ta karɓa kuma ta duba takardar hukuncin kotu, da ya shafi karar da ke tsakaninta da Shugaban Majalisar, Sanata Godswill Akpabio.

Shugaban kwamitin hulɗa da jama’a na majalisar Sanata Yemi Adaramodu ne ya bayyana hakan, a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a ranar Lahadi a Abuja.

A ranar 6 ga Maris, 2025, Majalisar ta dakatar da Sanata Natasha na tsawon wata shida bayan rikici da ya shiga tsakaninta da shugabancin majalisar kan sauya mata wurin zama.

Natasha ta garzaya kotun tarayya a Abuja, inda Mai Shari’a Binta Nyako ta umurci majalisar dattawa da ta janye dakatarwar.

Sai dai kotun ta kuma same Natasha da laifin raina kotu tare da hukunta ta da tara na naira miliyan biyar.

Adaramodu ya ce Majalisar ta riga ta nemi takardar hukuncin wato CTC tun ranar Litinin, kuma ba za ta ɗauki wani mataki ba har sai ta samu takardar don yin nazari.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata