Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaMajalisar dokokin jihar Benue ta dakatar da mambobinta biyar

Majalisar dokokin jihar Benue ta dakatar da mambobinta biyar

Majalisar dokokin jihar Benue ta dakatar da wasu mambobi biyar na kwamitinta kan kananan hukumomi, tsaro da al’amuran sarauta, bisa zargin sauya gaskiyar rahoton bincike da ya shafi shugaban karamar hukumar Otukpo, Hon. Maxwell Ogiri.

Sanarwar mai magana da yawun Kakakin Majalisar, Terver Zamber, ta bayyana cewa an dakatar da mambobin har na zaman majalisa uku saboda yunkurin kare shugaban karamar hukumar daga hukunci.

Wadanda aka dakatar sun hada da: Hon. Shimawua Terna da Hon. Mathew Damkor da Hon. Cephas Dyako da Hon. Moses Egbodo da kuma Hon. Isaac Echekliye.

Majalisar ta kafa wani sabon kwamiti na wucin gadi karkashin Hon. Ipusu domin sake nazarin zarge-zargen almundahana da rufe zauren majalisa da ake zargin shugaban Otukpo da aikatawa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata