Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiMajalisar wakilai ta amince da hukuncin shekaru 2 a gidan gyaran hali...

Majalisar wakilai ta amince da hukuncin shekaru 2 a gidan gyaran hali ga masu saye da sayar da kuri’u

Majalisar Wakilai ta amince da gyare-gyare masu tsanani ga dokar zabe, inda aka sanya hukunci mafi tsauri ga saye da sayar da kuri’u, wanda ya hada da aƙalla shekaru 2 a gidan gyaran hali ko tarar Naira miliyan 5, ko duka biyun, tare da hana mutum tsayawa takara na tsawon shekaru 10.

Hukunci mafi tsauri ya shafi saye da sayar da kuri’u da katin zabe, inda yanzu aka kara hukunci fiye da wanda ake da shi a baya na N500,000 ko shekaru biyu a gidan yari. An kuma amince da sabbin dokoki kan tura sakamakon zabe daga kowace rumfa ta hanyar na’urar IREV a lokaci guda da tattara sakamakon hannu, domin karfafa gaskiya da sahihancin zabe.

Bugu da kari, an kara hukunci ga shugabannin rumfunan zabe da suka karya ka’idoji wajen kirga, bayyana, ko aika sakamakon rumfa, inda sabon hukunci ya tanadi aƙalla tarar N500,000 ko watanni shida a gidan gyaran hali, ko duka biyun.

An amince da sakin kudaden zabe ga INEC aƙalla shekara ɗaya kafin babban zabe, da kuma amfani da katin zabe mai QR code don tabbatar da masu kada kuri’a kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata