Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiMajalisar wakilan Nijeriya ta katse zamanta na ranar Talata saboda muhawara kan...

Majalisar wakilan Nijeriya ta katse zamanta na ranar Talata saboda muhawara kan kasafin kudin 2026

Majalisar wakilan Nijeriya ta katse zamanta na ranar Talata sakamakon zazzafar muhawara kan kasafin kudin 2026

Jaridar Punch ta ruwaito cewa ba a samu gabatar da kuduri ko guda ba a zaman Talatar sakamakon daukar matakin, lamarin da ba a saba ganin irin sa ba.

Musayar yawu tsakanin ‘yan majalisar dai ya biyo bayan samun rabuwar kai game da yadda za a tafiyar da batun kasafin kudin Nijeriya na shekarar 2026.

Duk da cewa babu wata sanarwa a hukumance daga shugabancin majalisar, majiyoyi sun bayyana cewa tattaunawar ta mayar da hankali ne kan wa’adin da aka bai wa ministocin kudi, kasafi da tsare-tsare tare da akanta janar na kasar, kan biyan basusukan da ‘yan kwangila ‘yan asalin Nijeriya ke bi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata