Monday, April 6, 2026
HomeKetareMali ta haramta mujallar Jeune Afrique a duk fadin kasar

Mali ta haramta mujallar Jeune Afrique a duk fadin kasar

Gwamnatin kasar Mali ta haramta yadawa ko rarraba wa da ma siyar da mujallar Jeune Afrique a duk fadin kasar.

Hukumomin Malin sun dauki wannan mataki ne sakamakon zargin karya marar hujja da na bata sunan kasar da suka ce jaridar ta Jeune Afrique ta yi wa kasar akan matsalar man fetur

Haka zalika hukumomin Malin sun zargin da jaridar ta yi musu ba shi tushe balle makama, ta kuma nuna son rai a yayin hada rahoton da kuma nuna rashin sanin makamar aikin jarida

Hukumomin sun ce duk wanda aka samu da bujerewa umarnin to zai fuskanci hukuncin doka

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata