Gwamnatin kasar Mali ta haramta yadawa ko rarraba wa da ma siyar da mujallar Jeune Afrique a duk fadin kasar.
Hukumomin Malin sun dauki wannan mataki ne sakamakon zargin karya marar hujja da na bata sunan kasar da suka ce jaridar ta Jeune Afrique ta yi wa kasar akan matsalar man fetur
Haka zalika hukumomin Malin sun zargin da jaridar ta yi musu ba shi tushe balle makama, ta kuma nuna son rai a yayin hada rahoton da kuma nuna rashin sanin makamar aikin jarida
Hukumomin sun ce duk wanda aka samu da bujerewa umarnin to zai fuskanci hukuncin doka
