Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiMata biyu da ke tsare a hannun ‘yan bindiga sun haihu a...

Mata biyu da ke tsare a hannun ‘yan bindiga sun haihu a jihar Sokoto

Wasu mata biyu cikin mutum takwas da aka sace a kauyen Takatsaba da ke Karamar Hukumar Sabon Birni a Jihar Sokoto sun haifi jarirai namiji da mace yayin da suke tsare a hannun ’yan bindiga, makonni bakwai bayan sace su tare da wasu ’yan uwansu shida.

Wani dan uwan wadanda abin ya shafa ya ce maharan sun kai hari kauyen, sun yi ajalin wani dattijo sannan suka sace mutum takwas daga gida daya.

A cewarsa, an biya sama da Naira miliyan takwas daga cikin kudin fansa Naira miliyan goma da aka nema, yayin da uku daga cikin wadanda aka sace suka tsere kuma yanzu suna karbar magani a Sabon Birni.

Hakazalika, ya yi kira ga hukumomin tsaro su kara kaimi a yankin, amma kakakin rundunar ’yan sanda ta jihar ya ce ba su da rahoton faruwar lamarin saboda ba a kai musu kara ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata