Tsohon Shugaban Nijeriya, Goodluck Jonathan, ya bayyana cewa zama memba a Dandalin Dattawan Afrika ta Yamma (WAEF) shi ne babban dalilin da ya hana shi komawa siyasa kai tsaye ko mara baya ga kowace jam’iyya.
A cewar Jonathan, yayin taron cika shekaru 10 da kafa Goodluck Jonathan Foundation (GJF) da aka gudanar a Abuja, kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito, dokokin dandalin na WAEF sun wajabta wa membobinsu su kasance masu ajiye ra’ayin siyasa ko bangaranci a gefe.
Jonathan ya bayyana WAEF a matsayin mai tsarin da ke kai ziyara ƙasashe a lokacin zaɓe domin shawo kan duk wani alamar tashin hankali tun kafin ya rikide ya zama rikici baki ɗaya.
Ya kuma yi tir da abin da ya kira “tashanci a siyasar Nijeriya”, yana kira ga ’yan siyasa su gudanar da harkokinsu cikin ladabi, hikima da ɗa’a domin kare mutuncin ƙasa da dimokuraɗiyya.
Matsayin da nake da shi a kungiyar dattawan Yammacin Afrika ya sa na janye daga harkokin siyasa – Jonathan
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
