Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiMinistan Ilimi ya janye maganarsa tare da amincewa da yarjejeniyar kungiyar ASUU...

Ministan Ilimi ya janye maganarsa tare da amincewa da yarjejeniyar kungiyar ASUU ta 2009

Ministan Ilimi, Tunji Alausa, ya janye ikirarin da ya yi a baya cewa babu wata yarjejeniya mai tsakanin gwamnatin tarayya da ƙungiyar malaman jami’o’i ta Nijeriya ASUU, inda yanzu ya amince cewa yarjejeniyar 2009 ta FGN-ASUU tana nan daram.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, ministan ya bayyana cewa yarjejeniyar ta shekarar 2009 na nan a matsayin ingantacciya kuma mai ɗaurewa har zuwa yau.

Wannan karin haske ya biyo bayan jawabin da ya yi wa manema labarai a ranar Alhamis a Abuja, inda ya yi watsi da matsayar ASUU a matsayin takardar daftari kawai, yana mai jaddada cewa babu wata yarjejeniya da aka taɓa sanya hannu a kanta, abin da kungiyar ta yi gaggawar ƙalubalanta.

A cewar ministan, yarjejeniyar 2009 da 2011 da ASUU ke yawan ambato, “ba a taɓa sanya hannu a kansu ba, sai dai shawarwari ne da aka gabatar yayin tattaunawa.”

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata