Ministan tsaron Nijeriya, Christopher Musa, ya kira taron gaggawa da dukkan hafsoshin rundunonin soji ofishinsa domin tattauna yadda za a shawo kan hare-haren da ake kai wa sansanonin sojoji a yankin Arewa maso Gabas.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa manyan jami’an tsaron sun hada da babban hafsan tsaro Olufemi Oluyede, da babban hafsan sojin ƙasa, Waidi Shaibu, sauran sun hada da babban hafsan sojin sama, Sunday Aneke, da na sojin ruwa, Idi Abass.
Rahotanni sun ce taron ya biyo bayan sabbin hare-haren da ‘yan ta’adda suka kai kan sansanonin sojoji a jihar Borno, inda akalla kwamandoji uku masu manyan suka rasa rayukansu.
