Hedikwatar tsaron Najeriya ta bayyana cewa ta kama ‘yan ta’adda akalla 450, tare da ceto mutane 180 da aka yi garkuwa da su a cikin watan Satumban 2025.
Daraktan yada labaran rundunar Manjo Janar Markus Kangye ne ya bayyana haka a ranar Asabar, kamar yadda The Nation ta ruwaito.
A cewar sa, ‘yan ta’adda 39 sun zubar da makamansu tare da mika wuya ga jami’an soji, baya ga samun nasarar kwato tarin manyan makamai da alburusai a watan.
Kangye ya ce sojojin sun samu wannan gagarumar nasara ce karkashin shirye-shiryen hadin gwiwa da suka hadar da ‘Operation Hadin Kai’, ‘Operation Fansan Yamma’, ‘Operation Whirl Stroke’ ‘Operation Delta Safe’ da kuma ‘Operation Udo Ka’.
