Hukumar ICPC mai yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana cewa tana tsare da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai.
Hukumar ta ce El-Rufai yana hannunta har bayan an tashi aiki na ranar Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026.
A wata sanarwa da kakakin hukumar, J. Okor Odey, ya fitar, ICPC ta ce ana rike da shi ne dangane da bincike da take gudanarwa.
