Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiMutane 3 sun rasa rayukansu a wata gobarar tankar man fetur a...

Mutane 3 sun rasa rayukansu a wata gobarar tankar man fetur a jihar Kano

Mutane uku sun rasa rayukansu yayin da wani ya tsira da raunuka a wata gobara mabambanta da aka samu a jihar Kano a ranar Juma’a, kamar yadda hukumar kiyayewa da kashe gobara ta Jihar Kano ta sanar.

Gobarar ta farko ta faru ne da rana, kimanin karfe 1 na rana, lokacin da tankar mai mai dauke da lita 30,000 ta fadi a wajajen kasuwar Kura da ke hanyar Zaria.

A cewar hukumar, masu kashe gobara sun isa wurin nan da nan bayan samun kiran agaji daga tsohon jami’in Civil Defence, Danlami Muhammad. An samu mutane hudu da abin ya shafa; uku daga cikinsu sun mutu, yayin da mai napep ya tsira da rai.

Hukumar ta ce masu kashe gobara tare da jami’an ‘yan sanda da na kiyaye hadurra sun dakile wutar sannan suka mika gawarwakin ga ASP Ahmad Lawan na rukunin ‘yan Sanda na Kura. An tura motoci biyu na kashe gobara daga hedkwata da kuma ofishin Kura domin dakile gobarar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata