Kocin kasar Senegal, Pape Bouna Thiaw, ya ce zafin zuciya ne ya sa ya umarci ’yan wasansa su fice daga fili a wasan ƙarshe na kofin nahiyar Afirka AFCON da aka fafata da Moroko.
Thiaw ya bayyana hakan ne a wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Instagram, kamar yadda Premium Times ta ruwaito, bayan cece-kucen da ya biyo bayan hukuncin bugun fenariti da aka bai wa Moroko sakamakon duba VAR a ƙarshen wasan.
Lamarin ya faru ne lokacin da Senegal ta nuna rashin amincewa da hukuncin alkalin wasa, lamarin da ya sa ’yan wasan suka fice daga fili na ɗan lokaci kafin daga bisani su dawo su kammala wasan.
