Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiNa zo ne don na taimaki 'yan Nijeriya, ba zan cutar da...

Na zo ne don na taimaki ‘yan Nijeriya, ba zan cutar da kowa ba – Tinubu

 

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya tabbatar wa ‘yan kasar cewa ya zo mulki ne domin ya taimake su ba domin ya cutar da kowa ba. Shugaban ya bayyana hakan a yayin da yake jawabi ga yan kasar a yammacin Litinin din nan.

Tinubu ya kuma bayyana cewa ya san irin halin da ‘yan Nijeriya ke ciki tun bayan cire tallafin man fetur da gwamnatinsa ta yi. Sai dai ya ce babu wata mafita idan ba dauki wannan mataki ba, yana mai cewa idan da akwai wata hanya ta dabam domin ci-gaba da ya dauke ta, ya kauce wa janye tallafin.

Kawo yanzu dai shugaban ya ce gwamnatinsa ta yi nasarar adana sama da naira tiriliyan daya daga dakatar da biyan tallafin da ta yi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata