Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiNade-naden daraktoci a hukumar tattara haraji ya Nijeriya ya saba wa dokar...

Nade-naden daraktoci a hukumar tattara haraji ya Nijeriya ya saba wa dokar kafa hukumar – Daily Trust

Rahoton Daily Trust ya nuna cewa nadin daraktoci biyar daga cikin shida na Hukumar Tara Haraji ta Nijeriya (NRS) ya saɓa wa tanadin Sashe na 17 (1) na Dokar Kafa NRS ta 2025 da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanya wa hannu.

Dokar ta tanadi cewa Shugaban Ƙasa zai naɗa daraktoci shida, kowanne daga yanki ɗaya na ƙasar nan bisa tsarin juyawa da jerin jihohi a haruffa, tare da sharadin cewa shugaban hukumar da darakta ba za su fito daga jiha ɗaya ba. Sai dai bincike ya nuna cewa sai daraktar Kudu maso Kudu kaɗai, Iniabasi Akpan daga Akwa Ibom, ita kadai Ce ta dace da tanadin dokar.

A cewar rahoton, ya kamata nadin ya kasance daga Benue (Arewa ta Tsakiya), Jigawa (Arewa maso Yamma), Adamawa (Arewa maso Gabas), Abia (Kudu maso Gabas) da Ekiti (Kudu maso Yamma), amma an naɗa daraktoci daga wasu jihohi daban.

Ƙoƙarin jin ta bakin fadar shugaban ƙasa bai yi nasara ba, yayin da daraktan yada labarai na jam’iyyar APC ya ce ɓangaren zartaswa ne kaɗai ke da alhakin fadin wani abu gane da al’amarin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata