Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiNAHCON ta gargadi maniyyata Hajjin 2026 na Nijeriya kan yin rijista da...

NAHCON ta gargadi maniyyata Hajjin 2026 na Nijeriya kan yin rijista da wuri

By Fatima Aminu Dabo

Hukumar jin daɗin alhazai ta kasa NAHCON ta sanar da jadawalin aikin Hajjin 2026, inda ta bayyana cewa 20 ga Maris, 2026 ce ƙarshe wajen fitar da visa, tare da jaddada cewa ba za a yi ƙarin lokaci ba.

A cikin sanarwar da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ta ce za a rattaba hannu kan yarjejeniyar shirye-shirye da hukumomin Saudiyya a watan Nuwamba, 2025, yayin da ta sanya 8 ga Oktoba, 2025 a matsayin rana ta ƙarshe ta tura kuɗaɗen jihohi da masu gudanar da hajji domin tabbatar da gurabe.

NAHCON ta yi kira ga hukumomin jihohi da kamfanonin jigilar mahajjata da su bi wannan jadawali don guje wa matsaloli, tare da tabbatar da hajji mai tsari da kwanciyar hankali ga ’yan Najeriya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata