Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiNajeriya na cikin ƙasashe 10 a duniya da suka fi take haƙƙin...

Najeriya na cikin ƙasashe 10 a duniya da suka fi take haƙƙin ma’aikata – Binciken ICTU Global Index

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta bayyana rashin jin daɗinta kan yadda ƙasar ta ƙara faɗawa cikin jerin ƙasashen da ke da mummunan tarihin take haƙƙin ma’aikata a duniya.

Shugaban NLC, Comrade Joe Ajaero, wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Adewale Adeyanju, ya bayyana haka ne a lokacin taron shekara-shekara karo na 68 na ƙungiyar NECA (Nigeria Employers’ Consultative Association) da aka gudanar a birnin Lagos a ranar Laraba.

A cewarsa, sabon rahoton na ITUC Global Rights Index na 2025 ya sanya Najeriya cikin ƙasashe 10 a duniya da suka fi take haƙƙin ma’aikata.

Ajaero ya ƙara da cewa da yawa daga cikin take haƙƙin ma’aikata da rahoton ya ambata, na faruwa ne a cikin manyan kamfanoni da cibiyoyin kasuwanci da ke cikin ƙungiyar NECA.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata