Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiNAPTIP ta ceto mutane 221 daga hannun masu fataucin mutane a jihar...

NAPTIP ta ceto mutane 221 daga hannun masu fataucin mutane a jihar Jigawa

Hukumar da ke kula da hana fataucin mutane, NAPTIP ta jihar Jigawa ta ce ta ceto mutane 221 da aka yi fataucinsu cikin shekaru biyu da suka gabata.

Kwamandan hukumar a jihar, Malam Abdulladir Turajo, ya bayyana hakan a taron wayar da kai da aka gudanar a Kazaure, inda ya ce an maido da waɗanda aka ceto zuwa ga iyalansu tun bayan kafa ofishin hukumar a watan Yuli 2023.

A cewarsa, hukumar ta samu hukunta masu laifina sau biyu tare da gudanar da shirye-shiryen wayar da kai guda 175 a makarantu, kasuwanni, wuraren ibada da tashoshin mota a fadin jihar.

Taron wanda aka shirya tare da ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar Jigawa, na cikin shirin fadakarwa a matakin ƙananan hukumomi 27 na jihar, kuma an fara shi da yankin arewa maso yamma na jihar Jigawa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata