Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ‘yar Majalisar Dattawa daga jihar Kogi da aka dakatar, ta shigar da ƙara ga Majalisar Dattawa tana neman su girmama hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ta bayyana dakatarwar wata shida da aka yi mata a matsayin wuce gona da iri.
Kotun, a hukuncin da ta yanke a ranar 4 ga Yuli, ta umurci majalisar da ta duba yiwuwar dawo da sanatar kan kujerarta, tana mai cewa dakatarwar ta sabawa kundin tsarin mulki da kuma ‘yancin wakilcin jama’arta.
A cikin wata wasiƙa mai kwanan wata 11 ga Yuli, 2025, da lauyoyinta na M.J. Numa & Partners LLP suka tura wa majalisar, Sanata Natasha ta bukaci a cika duka sharuddan hukuncin da Mai Shari’a Binta Nyako ta yanke.
Ta kuma bayyana shirinta na komawa bakin aiki ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, tana mai cewa dakatarwar ta sabawa tsarin mulkin ƙasa.
Natasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
