Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiNijeriya ba za ta yarda a yi mata katsalandan kan tsaro ba...

Nijeriya ba za ta yarda a yi mata katsalandan kan tsaro ba – Martanin hedkwatar tsaro ga Jakadan Turkiyya

Hedkwatar tsaron Nijeriya ta bayyana cewa ƙasar na da cikakken ‘yanci da ikon yanke shawara da kanta, musamman a batutuwan tsaro da yaki da ta’addanci.

Wannan martanin na zuwa ne bayan wasu kalaman da Jakadan Turkiyya a Najeriya, Mehmet Poroy, ya furta a Abuja a ranar Talata, inda ya yi zargin cewa wasu mambobin ƙungiyar da gwamnatin Turkiyya ke kiran Fethullah Terrorist Organisation (FETO) na gudanar da ayyukansu a Nkjeriya karkashin sunan makarantu da cibiyoyin lafiya.

Amma yayin wani taron manema labarai a Abuja a ranar Alhamis, Daraktan huldar da jama’a na hedkwatar Manjo Janar Markus Kangye, ya bayyana cewa wannan zargi ba shi da tushe a hukumance a wajen rundunar.

Ya ƙara da cewa Nijeriya ba za ta saurari kowanne irin bayani daga waje ba, muddin bai da tushe a cikin bayanan leƙen asirin ƙasa da take tattarawa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata