Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiNLC ta bukaci gwamnatin tarayya ta gaggauta rage farashin man fetur

NLC ta bukaci gwamnatin tarayya ta gaggauta rage farashin man fetur

Kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta bukaci gwamnatin Nijeriya da ta rage karin farashin man fetur da tayi a yan kwanakin nan.

Bayanin hakan na a cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar kwadagon ta NLC ya fitar, Joe Ajaero, a Abuja, yana mai cewa  karin kudin ya kara ta’azzara talauci a duka fadin kasar nan, kuma babu wani fa’ida ta zahiri tattare da shi.

Sabon karin farashin man fetur din ya kai Naira 1,030 kan kowace lita a gidajen mai na kamfanin NNPCL mai kula da harkokin mai a Nijeriya.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata