Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaNNPP ta ce za ta ci zaben Kano a 2027 ko da...

NNPP ta ce za ta ci zaben Kano a 2027 ko da Gwamna Abba ya koma APC

Wani jigo a jam’iyyar NNPP Ladipo Johnson, ya bayyana kwarin gwiwar cewa jam’iyyar za ta lashe zaben Kano a 2027 ko da Gwamna Abba Kabir Yusuf fice daga cikinta tare da komawa APC.

 

Kalaman nasa sun zo ne a daidai gabar da Gwamnan ya gana da shugaban Nijeriya a fadarsa da ke Abuja a ranar Litinin 19 ga watan Janairun 2025.

 

A cewar Ladipo, ko kadan batun shirin ficewar Gwamnan daga NNPP ba ta girgiza su ba, kasancewar sun gina tubali mai kwari da zai taimaka musu wajen lashe zabe a jihar Kano da ke arewacin Nijeriya, kamar yadda Channels TV ya wallafa.

 

Duk da cewa ganawar Gwamna Abba da shugaba Tinubu ta ruruta batun komawar sa jam’iyyar APC, mai magana da yawunsa Sanusi Bature Dawakin Tofa ya ce ganawar tasu ta ta’allaka ne kan abubuwan da suka shafi kalubale, ayyuka da kuma ci-gaban jihar Kano.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata