Wednesday, April 8, 2026
HomeSiyasaObasanjo ya ce bai san takamaiman shekarunsa ba

Obasanjo ya ce bai san takamaiman shekarunsa ba

Tsohon Shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya ce bai san cikakkiyar adadin shekarunsa ba, yana dai kiyasta wa ne bisa ga abokan karatunsa da suka haura 90.

Jaridar Punch ta ambato shi a tattaunawa da Toyin Falola, ya bayyana cewa Obasanjo Presidential Library ɗakin karatun na adana tarihin rayuwarsa.

Tare da takardun makaranta, wasikun zamansa a kurkuku, rubuce-rubuce da sauran bayanai, domin kare tarihi da kuma ilmantar da masu zuwa gaba.

Obasanjo ya koka cewa rashin adana tarihi da bayanai yadda ya kamata na daga cikin matsalolin Najeriya, don haka ɗakin karatun nasa na da muhimmiyar rawa wajen gyara wannan gibin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata