Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiObasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa.

Rubutun da ba a san marubucinsa ba ya bayyana shi a matsayin mutum mai shekaru 84, alhali Obasanjo zai cika shekaru 89 a ranar 5 ga Maris, 2026.

Da yake magana a wajen taron bikin cikarsa shekaru 89 a Abeokuta, Jihar Ogun, Obasanjo ya bayyana masu yada labarin a matsayin marasa aikin yi, yana mai cewa Allah Ya tabbatar masa da tsawon rai da karfin ci gaba da ayyukansa.

Daga karshe kuma ya ce, yana nan daram kamar yadda aka saba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata