Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiOfishin jakadancin Amurka ya soke neman biza a Abuja saboda fargabar zanga-zanga

Ofishin jakadancin Amurka ya soke neman biza a Abuja saboda fargabar zanga-zanga

Ofishin Jakadancin Amurka a Nijeriya ya soke dukkan alƙawuran neman biza na ranar 4 ga Maris, 2026 a Abuja, sakamakon yiwuwar zanga-zanga da ka iya barkewa saboda rikicin Amurka da Iran.

Sanarwar da ofishin ya fitar ta ce akwai barazanar zanga-zanga a Babban Birnin Tarayya, don haka ta bukaci ’yan ƙasar Amurka da ke Abuja su zauna a gidajensu tare da kauce wa wuraren taro. Ta kuma ce za a tuntubi masu neman biza domin sake tsara musu sabuwar rana.

Matakin na zuwa ne bayan rahotannin mutuwar jagoran addinin Iran, Ali Khamenei, lamarin da ya kara tsananta rikicin da ke gudana a yankin Gabas ta Tsakiya.

Ofishin ya jaddada cewa sashen jakadanci na Abuja da ofishin jakadanci a Legas za su ci gaba da aiki, tare da shawartar jama’a su rika bibiyar shafinsu domin samun karin bayani.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata