DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Sunday, April 12, 2026
Home Blog Page 115

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar.

Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya ta damu da yadda Amurka ta yi hanzarin fitar da wannan matsayi bisa bayanan da ba su da tushe. Ya ce matsalolin tsaro a Nijeriya sun shafi Musulmai da Kiristoci baki ɗaya, ba wai rikicin addini ba ne.

DCL Hausa ta ruwaito cewa Ministan ya jaddada cewa rikicin manoma da makiyaya a Plateau da Benue ya samo asali daga tsoffin matsaloli da canjin yanayi da fari suka haifar da ƙara taɓarɓarewar. Ya ƙara da cewa gwamnati tana ƙarfafa haɗin kai da ƙasashen duniya, ciki har da Amurka, don kawo ƙarshen ta’addanci a yankin Sahel da Nijeriya baki ɗaya.

A cewarsa, hadin gwiwar da ke tsakanin Nijeriya da Amurka ya haifar da samun jiragen Super Tucano da ake amfani da su a yaƙin ta’addanci, tare da shirin karɓar sabbin jiragen yaƙi na AH-1Z Viper domin ƙarfafa rundunar sojojin sama.

Hakazalika, ya ce gwamnatin Tinubu tana bin duk hanyoyin diflomasiyya da siyasa don gyara kuskuren fahimtar da gwamnatin Amurka ta yi, tare da tabbatar da cewa ’yancin addini da rayuwar kowane ɗan ƙasa za su kasance a ƙarƙashin kariya da doka.

PDP ta kafa kwamitin sulhu tsakanin bangarorin da ke rikici a jam’iyyar

0

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP ya kafa kwamiti na musamman domin sasanta dukkan bangarorin da ke cikin sabani kafin babban taron zaben shugabanni na kasa da za a gudanar a Ibadan, Jihar Oyo, a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba, 2025.

Wannan mataki ya fito ne daga wani taron gaggawa da kwamitin ya gudanar a ranar Laraba, 5 ga watan Nuwamba, 2025, an Abuja.

Kwamitin sulhun mai mutum shida zai kasance karkashin jagorancin Ambasada Hassan Adamu daga Arewa maso Gabas, tare da Cif Mike Oghiadomhe daga Kudu maso Kudu a matsayin sakatare. Ana sa ran kwamitin zai mika rahotonsa kafin 11 ga watan Nuwamba, 2025.

Kwamitin amintattun ya yaba da kokarin kwamitin riko karkashin jagorancin Damagum da sauran kungiyoyin jam’iyyar wajen kwantar da rikice-rikicen cikin gida, tare da gode wa kotun Jihar Oyo bisa hukuncin da ta yanke na amincewa da jam’iyyar ta gudanar da nata al’amura ba tare da katsalandan ba.

‘Yan sanda sun kama matar da ta sace kanta don ta karbi kudin fansa daga mijinta a Nijeriya

0

Rundunar ‘yan sandan jihar Edo ta kama wata mata mai suna Chioma Success mai shekaru 27 bisa zargin shirya garkuwa da kanta don karɓar kudin fansa daga mijinta.

Mai magana da yawun rundunar, ASP Eno Ikoedem, ta ce mijin Chioma, Paul Adaniken, ya kai rahoto cewa matarsa da ɗansa sun ɓace, inda daga baya aka kira shi da wata lamba da ba a sani ba ana neman fansar Naira miliyan bitar.

Bincike ya gano cewa ɗan’uwan matar, Osita Godfrey, da wani abokinsu Martins Chidozie, sun taimaka wajen shirya satar. Daga baya Chioma ta amsa cewa ita ce ta tsara komai don ta karɓi kuɗi daga mijinta.

‘Yan sanda sun ce an kwato kudin fansar kuma an mika lamarin ga sashen binciken manyan laifuka na jihar don ci-gaba da bincike da gurfanarwa.

Ci-gaban tattalin arzikin Nijeriya bai kawo saukin rayuwa ga ‘yan kasar ba – Sanusi Lamido Sanusi

0

Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya gargadi cewa ci-gaban tattalin arzikin Nijeriya ba ya fassaruwa zuwa ingantacciyar rayuwa ga ’yan ƙasar.

Sanusi ya bayyana hakan ne a wani taron kasa da kasa na Afirka kan kudin Musulunci da aka gudanar a Legas, inda ya ce ƙididdigar ci-gaban tattalin arziki da hauhawar farashi ba su nuna ainihin halin da talakawa ke ciki ba.

A cewarsa, duk da cewa GDP na ƙaruwa, idan ya takaita ne ga wasu kawai, yawancin jama’a za su ci gaba da fama da talauci.

Sanusi ya shawarci cibiyoyin kuɗin Musulunci da su mai da hankali wajen tallafawa kananan ’yan kasuwa, manoma da ma’aikata a yankunan karkara, yana mai cewa hakan ne kaɗai zai tabbatar da ingantacciyar rayuwa ga jama’a.

Tinubu ya nemi amincewar majalisa da ciyo bashin fiye da Naira tiriliyan daya

0

Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya nemi amincewar majalisar dattawa don karbo rancen Naira tiriliyan 1.15 daga kasuwar cikin gida domin cike gibin kasafin kuɗin shekarar 2025.

Wannan buƙata ta kasance cikin wasikar da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya karanta a zauren majalisa yayin zaman da aka gudanar a ranar Talata.

A cikin wasikar, Tinubu ya bayyana cewa rancen ya zama dole don samar da kuɗin da za a yi amfani da su wajen aiwatar da manyan shirye-shiryen gwamnati da ayyukan raya ƙasa.

A cewarsa, wannan tsari na rance wani ɓangare ne na dabarun gwamnati don farfaɗo da tattalin arziƙi, samar da ayyukan yi, da tabbatar da ci-gaban ƙasa.

Majalisar ta tura buƙatar zuwa kwamitin bashi na cikin gida da na ƙasashen waje domin yin nazari da bayar da rahoto cikin mako guda.

Amurka ta mayar wa China da martani kan gargadin harin soja a Nijeriya

0

Wani ɗan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore, ya caccaki China saboda gargadin da ta yi wa Washington kan yiwuwar harin soja a Nijeriya bisa zargin kisan Kiristoci, yana mai cewa Beijing ba za ta tsoma baki a siyasar Amurka ba.

Moore ya goyi bayan shugaba Donald Trump, yana mai cewa Amurka na da nauyin kare Kiristoci masu fuskantar zalunci, kuma ya zargi China da rashin gaskiya kan batun ‘yancin dan Adam, yana cewa ba za a karɓi nasiha daga “gwamnatin kama-karya” ba.

China ta gargadi Amurka da ta daina tsoma baki a harkokin tsaron Nijeriya, inda ta bayyana goyon bayanta ga gwamnatin Nijeriya.

Sai dai gwamnatin kasar China, ta gargaɗi Trump da ya mutunta ikon da ‘yancin Nijeriya, tare da kauce wa duk wani yunkurin tura sojojin Amurka zuwa ƙasar.

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

0

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald Trump kan zargin kisan Kiristoci a kasar.

Trump ya yi wannan furuci ne bayan da Amurka ta sanya Nijeriya cikin jerin “kasashen da ke da damuwa ta musamman” saboda zargin wariyar addini, lamarin da ya jawo musayar yawu a tsakanin jakadun kasashen biyu.

Da yake jawabi a zauren majalisar a ranar Talata, shugaban majalisar dattawan Godswill Akpabio ya ce batun na da nasaba da manufofin diflomasiyya, don haka sai sun tuntubi gwamnatin tarayya kafin su dauki matsaya, sannan kuma kalaman Trump sun dogara ne da “tsohon rahoto na shekarar 2010” wanda bai yi daidai da halin da ake ciki a yanzu ba.

A cewarsa, matsalar tsaro a Nijeriya ba ta da alaka da addini, inda ya ce Musulmai da Kiristoci duka na fuskantar hare-hare iri daya daga ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga.

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

0

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a yankin suna da alaka da halaka wasu mabiya addini, tana mai jaddada cewa ta’addanci yana shafar kowa ba tare da bambancin addini ko kabila ba.

A sanarwar da ta fitar a ranar Talata, ECOWAS ta bayyana cewa kungiyoyin ta’addanci na kai hare-hare a kasashe da dama ciki har da Nijeriya, inda ake hallaka fararen hula ba tare da bambanci ba.

Kungiyar ta yi kira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran ƙasashe abokan hulɗa da su cigaba da tallafa wa kasashen yankin wajen yaki da tsattsauran ra’ayi da ta’addanci.

Sanarwar ta zo ne bayan shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana Nijeriya a matsayin “ƙasa mai damuwa ta musamman,” bisa zargin cewa ana barazana ga Kiristoci, abin da gwamnatin Nijeriyar ta musanta.

Shugaba Tinubu ya nemi majalisa ta tabbatar da sabon minista daga jihar Enugu

0

Shugaba Bola Tinubu ya aika wa majalisar dattawan Nijeriya wasikar neman tantancewa da tabbatar da Dr. Kingsley Tochukwu Ude, babban lauya daga Jihar Enugu, a matsayin sabon minista.

Shugaban majalisar dattawan, Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar a zaman da aka gudanar ranar Talata, inda ya mika sunan Ude ga kwamitin tantancewa don ci-gaba da nazari.

Nadin ya biyo bayan murabus din tsohon ministan kimiyya da fasaha, Uche Nnaji, wanda ya ajiye aiki saboda rikicin takardun karatu da na yi wa kasa hidima wato NYSC.

Dr. Ude, wanda ke rike da mukamin kwamishinan shari’a na jihar Enugu, zai maye gurbin Nnaji a majalisar zartarwa ta Tinubu.

Kotu ta ba jam’iyyar PDP izinin gudanar da taronta na kasa a Ibadan

0

Babbar kotun jihar Oyo da ke Ibadan ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a A. L. Akintola, ta bai wa jam’iyyar PDP damar gudanar da babban taronta na kasa da aka shirya yi a ranakun 15 da 16 ga watan Nuwamban 2025, a filin wasan Lekan Salami da ke Ibadan.

Hukuncin ya biyo bayan ƙarar da wani ɗan takara, Folahan Malamo Adelabi, ya shigar a kotu yana neman a tabbatar da bin jadawalin da jam’iyyar ta fitar tare da hana PDP da jami’anta yin wani abu da zai iya katsewa ko hana taron.

Mai shari’a Akintola ya kuma umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta Nijeriya INEC, da ta tura masu bibiya don tabbatar da gaskiya da bin doka a taron.

Hukuncin ya bai wa Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, wanda shi ne shugaban kwamitin shirya taron damar kammala shirye-shiryen da suka hada da halartar wakilai fiye da 3,000 daga fadin kasar.