Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana gamsuwarsa kan yadda ake gudanar da zaɓen kananan hukumomi cikin lumana a fadin Abuja, duk da korafin ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a a wasu sassan birnin.
Da yake magana bayan zagayen sa ido da ganawa da masu zaɓe, Wike ya ce yanayin tsaro ya kasance cikin kwanciyar hankali, yana mai danganta hakan da kokarin jami’an tsaro.
Ministan ya ƙara da cewa a irin wannan zaɓen da ba na gama-gari ba, ana yawan samun ƙarancin mahalarta, amma abin da ya fi muhimmanci shi ne an gudanar da zaɓen cikin lumana ba tare da tashin hankali ba.
Dangane da kalaman Sanata Ireti Kingibe wadda ta soki takaita zirga-zirga a matsayin kama-karya, Wike ya ce bai kakaba dokar hana fita ba.
FCT na da sama da masu rajista miliyan 1.5 da ake sa ran za su zabi shugabannin kananan hukumomi shida—Abuja Municipal, Bwari, Gwagwalada, Kuje, Abaji da Kwali—tare da kujeru 68 da ake takara, ciki har da shugabanci shida da kujerun kansiloli 62.