Tuesday, April 7, 2026
Home Blog Page 35

Gwamnatin Kano ta buƙaci mataimakin gwamna ya ajiye muƙami

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya buƙaci Mataimakin Gwamna Aminu Abdussalam Gwarzo da ya yi murabus idan ba zai iya ci gaba da tafiya da gwamna Abba Kabir Yusuf a sabon tsarin siyasa ba.

Waiya ya bayyana hakan ne yayin shirin kai tsaye a Muhasa Radio, inda ya ce sabanin siyasa a matakin koli na gwamnati na iya lalata amincewa da tafiyar da mulki, musamman ganin cewa mataimakin gwamnan na rike da muƙamin Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi.

Ya ce kamar yadda wasu kwamishinoni suka yi murabus saboda rashin jin daɗi, hakan ya dace mataimakin gwamnan ma ya ɗauki mataki cikin mutunci idan ba ya kan tafarkin siyasar gwamnan.

Waiya ya jaddada cewa shugabanci na bukatar haɗin kai da amincewa, yana mai gargadin cewa shakku na iya tasowa idan babban jami’in yana gwamnati amma yana bin wata hanyar siyasa ta dabam.

Iyabo Obasanjo ta shiga jam’iyyar APC

‘Yar tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo, Iyabo Obasanjo, ta koma siyasa bayan kusan shekaru 15, inda ta shiga jam’iyyar APC a Jihar Ogun gabanin zaɓen 2027.

Majiyoyi sun shaida wa Daily Trust cewa tsohuwar sanata da ta wakilci Ogun ta tsakiya a 2007 – 2011, ta kammala rajistar jam’iyyar APC a Ibogun, Ward 11, ƙaramar hukumar Ifo, yayin atisayen rijistar jam’iyyar da ake yi ta yanar gizo.

Iyabo, wacce kwararriyar masaniyar cututtuka (epidemiologist) ce kuma tsohuwar Kwamishiniyar Lafiya ta Ogun, ta sha kaye a yunƙurin sake komawa majalisa a 2011, kafin ta koma Amurka inda ta kai matsayin farfesa a harkar ilimi.

Rikicin masarautar Kano zai kawo ƙarshe – gwamnatin jihar

Gwamnatin Jihar Kano ta tabbatar da cewa rikicin da ya dabaibaye batun masarautu a jihar zai samu waraka cikin lumana nan ba da jimawa ba.

Kwamishinan yaɗa labarai da Harkokin cikin gida Ibrahim Waiya ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a Kano, inda ya ce gwamnati ta ɗauki matakai masu ƙarfi domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali mai ɗorewa.

Waiya ya jaddada cewa gwamnati na shirin tattaunawa da dukkan masu ruwa da tsaki, tare da bin doka, mutunta cibiyoyin gargajiya da kuma kare muradun al’ummar Kano baki ɗaya.

Ya buƙaci al’ummar Kano su kwantar da hankalinsu tare da tabbatar da cewa gwamnati na ci gaba da mayar da hankali kan haɗin kai, ci gaba da shugabanci nagari.

Kwamishinan ya ce za su tabbatar da gaskiya da zaman lafiya a jihar kamar yadda jaridar Daily Nigerian ta tattaro.

An yi wa wasu magidanta hukuncin aikata masha’a a kasar Indonesia

Kotun shari’ar musulunci a lardin Aceh na Indonesia ta yi wa wani namiji da wata mata bulala 140 kowanne a bainar jama’a, bisa laifin shan giya da kuma lalata ba tare da aure ba.

Bulalar ta gudana ne a wani fili a ranar Alhamis, inda jama’a da dama suka hallara.

Matar ta suma bayan kammala hukuncin, lamarin da ya sa aka kai ta asibiti.

Shugaban ‘yan sandan Shari’a na Banda Aceh Muhammad Rizal ya ce kotun Shari’a ta yanke musu hukuncin bulala 100 kan zina da kuma 40 kan shan giya, lamarin da ake ganin na daga cikin mafi tsauraran hukunci tun bayan aiwatar da dokar Shari’a a Aceh a shekarar 2001 bayan samun ikon cin gashin kai na musamman.

Aceh ita ce kadai a Indonesia ke aiwatar da dokar Shari’a, inda haramun ne yin jima’i tsakanin marasa aure.

Jimillar mutane shida ne aka hukunta a ranar, ciki har da wani jami’in ‘yan sandan Shari’a da budurwarsa da aka kama a wani wuri na kashin kai; wanda suka sha bulala 23-23 kamar yadda rahoton AFP ya tabbatar.

CAF ta dakatar da kocin Senegal Pape Thiaw wasanni biyar da tara

Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF ta dakatar da kocin Senegal, Pape Thiaw, wasanni guda biyar tare da cinsa tarar dala $100,000, bisa zargin aikata rashin da’a a yayin wasan ƙarshe na gasar kofin Afrika AFCON, da aka buga tsakanin Senegal da Morocco.

Rahotanni daga CAF sun nuna cewa an dauki matakin ne bayan da Thiaw ya umurci ‘yan wasansa su fice daga fili yayin wasan karshe da Morocco, abin da hukumar ta bayyana a matsayin saba wa dokokin wasanni da cin mutuncin gasar.

An kai farmaki a filin jirgin sama na birnin Yamai a Jamhuriyar Nijar

0

A Jamhuriyar Nijar wasu mutane da ba a san ko su wanene ba sun yi ruwan bama – bamai daga nesa zuwa filin tashi da saukar jiragen saman birnin Yamai.

DW Hausa ta rawaito cewa harin ya soma ne da misalin karfe 12 na dare da ‘yan mintoci har ya zuwa kusan karfe daya na safiyar Alhamis.

Amma rahotanni sun ce tuni jami’an tsaron kasar ta Nijar cikin gaggawa suka shawo kan matsalar, inda jama’a a cikin unguwanni musamman na kewayen filin jirgin saman na Yamai suka kasance cike da rudani.

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

0

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu dace ba.

Martanin ya biyo bayan furucin Atiku a wani taron ƙaddamar da littafi a Abuja a ranar Talata, inda ya bayyana gwamnatin APC a matsayin mummunar gwamnati mafi muni da ya taɓa gani cikin kusan shekaru 40 da yake a harkar siyasa, yana mai cewa ta fi ma gwamnatocin soja illa.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Laraba, mai ba Tinubu shawara kan harkokin yada Labarai Sunday Dare, ya zargi Atiku kalaman cin mutuncin ’yan Nijeriya.

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

0

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar mataki na ƙarshe.

An yanke wannan shawara ne a zaman Majalisar na ranar Laraba, bayan tattaunawa kan rahoton kwamitin majalisar dattawa kan harkokin zaɓe, wanda aka gabatar ba tare da halartar shugaban kwamitin ba, Sanata Simon Lalong.

Majalisar ta amince a janye muhawarar a wannan lokaci, tare da ci gaba da duba dokar ranar Alhamis, sannan majalisar ta kuma shiga zaman sirri domin tattauna muhimman batutuwan da ke cikin kudirin, ganin irin tasirin da gyaran dokar zai iya yi ga zaɓuka masu zuwa.

Tinubu da Kashim Shettima za su sake cin zaɓe tare a 2027 — Gwamna Sule

0

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya bayyana ƙwarin gwiwarsa cewa Shugaba Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shettima za su sake lashe zaɓen 2027 tare a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Daily Nigerian ta rawaito Gwamna Sule na fadin hakan ne a ranar Asabar yayin wani taro da aka gudanar a Jos da ke jihar Filato, domin murnar sauya sheƙar Gwamnan Plateau, Caleb Mutfwang, zuwa APC.

A cewarsa, shigar Gwamna Mutfwang APC ta kara karfin jam’iyyar a yankin Arewa ta Tsakiya, lamarin da zai ƙara mata ƙarfi a babban zaɓen 2027.

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf zai yi nadamar barin mu – Kwankwaso

0

Jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce yana da tabbacin cewa Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, tare da wadanda ke tare da shi, za su yi nadamar ficewa daga jam’iyyar NNPP.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne bayan da Gwamna ya koma jam’iyyar APC, lamarin da ya ce ya ba mutane da dama mamaki har da shi, ya ce a farko ma ya dauka kamar mafarki yake yi ganin yadda al’amura ke tafiya.

A ranar Litinin 26 ga Janairu, 2026, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sauya sheƙa zuwa APC, bayan da ya sanar da murabus dinsa daga NNPP a ranar Jumma’a 23 ga Janairu, 2026, kasa da shekaru uku da lashe zaben gwamnan Kano a karkashin jam’iyyar.