DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Monday, April 13, 2026
Home Blog Page 394

Akwai shawarar da muke shirin bayarwa na kara harajin VAT zuwa 10% a Nijeriya – Kwamiti

Kwamitin shugaban kasa na farfado da tattalin arzikin Nijeriya ya ce akwai wata shawara da suke shirin badawa ga majalisar dokoki ta kara harajin VAT daga 7.5% zuwa 10%.
Shugaban kwamitin Taiwo Oyedele ya sanar da hakan a wata zantawa da shi a gidan talabijin na Channels.
Sai dai shugaban kwamitin ya ce su na nan su na duba yiwuwar jimilce harajin da ake da su waje daya domin sake yin bita a rage musu yawa a kasar.
Oyedele ya ce wannan shawara da suka rubuta za su hannanta ta ga majalisar dokokin Nijeriya domin duba abin da zai yiwu

Shugaba Tinubu na aiki ba gajiyawa don tsaro ya inganta a Nijeriya – Kasshim Shettima

Mataimakin Shugaban kasa Sanata Kasshim Shettima ya ce shugaban kasar ba ya wasa da duk wani abu da ya danganci sha’anin tsaron Nijeriya.
Sanata Kasshim Shettima ya ce Shugaba Tinubu na aiki kan jiki, kan karfi don ganin tsaron lungu da sakon Nijeriya ya inganta ta yadda harkoki za su koma yadda ya kamata.
Da ya ke magana a fadar shugaban kasa, a lokacin da ya karbi bakuncin jagorancin kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya NAN, Sanata Kasshim Shettima ya bukaci da a hada hannu waje daya don magance matsalolin tsaron da ake fama da su.
Mataimakin Shugaban kasar ya bukaci da a yi wa matsalar taron-dangi don ganin an magance ta cikin kankanin lokaci.

Babu wani tsamin danganta tsakanin Shugaba Tinubu da Mataimakinsa Kasshim – Fadar Shugaban kasa

Fadar Shugaban Nijeriya ta sa kafa ta shure rade-radin da ke yawo cewa akwai tsamin danganta tsakanin Shugaba Tinubu da Mataimakinsa Kasshim Shettima.
A cikin wata sanarwa daga mataimaki na musamman kan kafafen yada labarai a ofishin Mataimakin Shugaban kasa, Stanley Nkwocha, ta ce Sanata Kasshim Shettima na samun dukkanin goyon baya da hadin kan da ake bukata wajen tafiyar da gwamnati daga bangaren Shugaba Tinubu.
Nkwocha ya musanta cewa akwai sagwangwanin rashin jituwa a tsakanin shugabannin biyu, yana mai cewa Sanata Kasshim Shettima mutum ne mai biyayya kuma ana damawa da shi a dukkanin harkokin tafiyar da mulkin Nijeriya.
A cikin sanarwar bikin cika shekaru 58 a duniya na Sanata Kasshim Shettima, Stanley ya bayyana wadannan rade-radi da cewa ba su da tushe bare makama ya kuma bukaci mutane su yi watsi da su.

Wike zai gurfana gaban kwamitin ladabtarwa bisa zargin yi wa PDP zagon-kasa na “Anti Party”

 

Jam’iyyar PDP ta gayyaci ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, bisa zargin yi ma jam’iyyar zagon-kasa.

Mataimakin sakataren yada labarai na Jam’iyyar na kasa, Ibrahim Abdullahi, ne ya bayyana haka a ranar Litinin a wani shiri na gidan Talabijin na Channels mai suna Sunrise Daily.

Abdullahi ya bayyana cewa an gayyaci Wike a gaban kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar PDP karkashin jagorancin Tom Ikimi wanda kwamitin ayyuka na jam’iyyar ya kafa.

Nijar na shirin gina wata sabuwar matatar mai a jihar Dosso

 

Wata tawagar hadin gwiwar wasu ma’aikatun Nijar karkashin jagorancin sabon ministan mai, ta kai ziyarar aiki domin gani da ido na wurin da za’a gina sabon kamfanin matatar mai a cikin jihar Dosso.

Ana sa ran sabuwar matatar man za ta rika tace ganga dubu 30 a ko wace rana a tashin farko kafin daga bisani a fadada zuwa dubu 100 a kowace ranar.

Ko baya ga matatar man ma akwai kuma babban cibiyar samar da wutar lantarki a jihohin Tillaberi Dosso da babban birnin Yamai domin rage dogaro da na ketare inji hukumomin.

An kama hedimasta da ake zargin ya cefanar da kadarar makarantarsa a Kano

 

Hukumar Korafe-korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC) ta kama shugaban makarantar firamare ta Gaidar Makada da ke karamar hukumar Kumbotso bisa zargin sayar da kadarorin makarantar.

Hakan na a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Kabir Abba Kabir, ya fitar ranar Asabar. Yana mai ce wa kamen ya biyo bayan bayanan sirri da hukumar ta samu na sayar da muhimman kadarorin makaranta ba bisa ka’ida ba.

Ya kara da cewa hukumar na binciken lamarin, kuma ana kokarin kwato kadarorin da aka salwantar.

Mun sa a binciki dalilin tashin gobara a gidan gwamnati – Gwamnan Katsina Dikko

Gwamnan jihar Katsina ya kafa kwamitin da zai gaggauta bincikar dalilin tashin gobara a wani sashe na gidan gwamnatin jihar a Katsina.
Gobarar da ta tashi a sanyin safiyar Litinin, ta lalata karamin dakin taro (Mini Chamber) da ke kusa da ofishin Gwamnan jihar.
Sai dai jami’an kashe gobara na gwamnatin tarayya da na jiha sun yi kokari wajen dakile wutar kada ta bazu zuwa sassan gidan.
Kwamitin da aka kafa din ne ake kyautata zaton zai gano musabbabin tashin wannan gobara.
A cikin wata sanarwa da Abdullahi Aliyu Yar’adua, daraktan yada labaran ofishin sakataren gwamnatin jihar ya sanya wa hannu, ta ce an dora wa kwamitin alhakin gano dalilin tashin gobarar da irin barnar da ta yi da sakacin da ya jawo tashinta da kuma ba da shawarwarin yadda za a magance afkuwar hakan a gaba.
‘Ya’yan kwamitin sun hada da shugaban ma’aikatan gwamnatin jihar Katsina, kwamishinan ayyuka, gidaje da sufuri, kwamishinan kasafin kudi, kwamishinan shari’a, kwamishinan tsaron cikin gida da kwamishinan yada labarai da sauransu.

Gobara ta tashi a gidan gwamnatin jihar Katsina

 

Gobara ta tashi da sanyin safiyar Litinin, ta kone wani sashe na babban dakin taro na gidan gwamnan jihar Katsina.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa babban dikin taron (red chamber)na  kusa da ofishin gwamnan jihar Malam Dikko Umaru Radda inda ya ke ganawa da muhimman mutane.

Ya zuwa hada wannan rahoto babu wani takamaiman musabbabin tashin gobarar da barnar da ta yi.

Atiku, Obi da Kwankwaso na tattaunawar dunƙulewa waje daya in ji PDP

 

Manya-manyan ‘yan adawa uku a Nijeriya na tattaunawa kan yiwuwar hadaka gabanin zaben shugaban kasa na shekarar 2027.

Mataimakin kakakin jam’iyyar PDP na kasa Ibrahim Abdullahi ne ya bayyana hakan a gidan talabijin na Channels a ranar Litinin.

Abdullahi ya ce, za su ajiye muradun kashin kansu a gefe su kulla kawance mai karfi don ceto Nijeriya a cikin kangin da jam’iyyar APC ta cefa kasar a shekarar 2027.

Likitoci sun dakatar da yajin aikin gargadi a Nijeriya

0
Kungiyar likitoci a Nijeriya ta dakatar da yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai da ta shiga a ƙasar.
Kungiyar ta fara yajin aikin ne a ranar Litinin 26 ga watan Agusta saboda sace wani dan kungiyar mai suna Dokta Ganiyat Popoola-Olawale. 
Kungiyar ta ce ta yanke shawarar dakatar da yajin aikin ne domin jawo hankalin masu ruwa da tsaki don ganin an sako dan kungiyar da aka sace cikin gaggawa.