DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Sunday, April 12, 2026
Home Blog Page 400

An kafa cibiyoyin samar da lantarki a wasu manyan jami’o’in Nijeriya, in ji ministan makamashi

Gwamnatin tarayya ta hanyar hukumar wutar lantarki sanya cibiyar samar da lantarki a manyan jami’o’i shida na tarayya, a matsayin wani yunkuri na samar da ingantacciyar wutar lantarki a muhimman bangarori ga al’umma.
Hukumar ta bayyana cewa ta samu gagarumin ci gaba wajen bunkasa ayyukan samar da wutar lantarki a Najeriya.
Wannan ya biyo bayan wata tattaunawa da daraktan hukumar, Abba Abubakar Aliyu, ya yi da ministan kudi kuma ministan tsare-tsare na tattalin arziki, Wale Edun.
Jami’o’in sun hada da jami’ar Abuja, jami’ar Maiduguri, jami’ar koyon dabarun aikin gona ta Michael Okpara da ke Umudike, jami’ar tarayya ta Gashua a Yobe, jami’ar ta tarayya da ke Abeokuta, da kuma kwalejin tsaro ta Najeriya da ke Kaduna.

Gwamnatin Shugaba Tinubu a Nijeriya za ta kafa sassan kula da tsofaffi

Gwamnatin tarayya ta ce ta kafa aƙalla wuraren kula da tsofaffi guda 40 da aka tanadar musamman don kula da tsofaffi a cikin Ma’aikatu, Sassa da Hukumomi daban-daban guda 40, tana mai cewa ba za a iya barin wata hukuma ko ma’aikata guda ɗaya ta rike dukkan al’amuran da suka shafi tsufa ba.
Duk da cewa gwamnati ba ta bayyana jerin ma’aikatun da aka kafa wadannan sashen ba, amma ta yi gargaɗi kan nuna wariya da ƙyamar tsofaffi a sassa daban-daban, tana mai cewa tsufa abu mai kyau da ya kamata a daraja, ba a raina ba.
Shugabar cibiyar kula da tsofaffi ta kasa (NSCC), Dr Emem Omokaro, ce ta bayyana wannan an Abuja yayin wani taron horarwa na farko don tabbatar kwarewar a bangaren kula da tsofaffi.

Za a bude sashen da zai rika duba lafiyar shugaban kasa da sauran manyan kasa a babban asibitin Nijeriya da ke Abuja

Asibitin kasa da ke Abuja zai bude wani sashe na musamman wanda zai kula da shugabanni, manyan jami’an gwamnati, da sauran shahararrun mutane dake ciki da wajen kasar.
Babban daraktan asibitin, farfesa Mahmud Raji, ya bayyana hakan jiya a Abuja yayin da ya jagoranci wata tawaga zuwa hedkwatar Media Trust Group.
Farfesa Muhammad ya ce za a gina wani gidan zama ko masauki da aka hade da sashen na musamman wanda zai kasance kamar otal mai tauraro biyar ko bakwai domin kula da dukkan nau’ikan manyan baki.
Farfesa Raji ya kuma ce sashen na musamman zai samu dakin gwaje-gwaje na ilimin guba, yana mai cewa a halin yanzu babu wani asibitin gwamnati da ke da irin wannan dakin gwaje-gwajen domin gwajin guba daga abinci ko muhalli a yayin gaggawa ga shugabannin da ke ziyara.

Kafanin kasar China ya sake kwace jirgin Najeriya a Canada

Kamfanin Zhongshang Fucheng industrial investment Ltd, wani kamfani daga kasar China da ake rikicin kwace jiragen sama uku na shugaban kasa a kasar Faransa da wasu kadarori a wasu kasashen, ya kwace wani jirgin na Najeriya a kasar Canada.
Wannan na zuwa ne bayan kwace jiragen sama uku na shugaban kasa da wata kotu a Faransa ta yi a madadin Zhongshan Fucheng, saboda wata takaddama tsakaninsa da gwamnatin jihar Ogun.
Kamfanin ya bayyana cewa ya yanke shawarar sakin daya daga cikin jiragen ukun domin nuna kyakkyawar niyya, mussamman a wani taro da aka shirya tsakanin shugaba Bola Tinubu da takwaransa na Faransa, Emmanuel Macron.
A ranar Litinin, Tinubu ya tafi Faransa a kan jirgin Airbus A330 da aka saki, duk da takaddamar da ta taso game da sayensa, bayan kamfanin na kasar Sin ya saki jirgin.
Kamfanin na kasar Sin ya samu sauyin mallakar takardun jirgin Bombardier 6000 nau’in BD-700-1A10 daga hukumomin Canada a Montreal, watanni kadan bayan wata kotu a Quebec ta yanke hukuncin da ya ba Zhongshang damar kwace jirgin daga hannun Najeriya.

Zanga-zangar rashin Sarkin Gobir, ta sa gwamnatin jihar Sokoto kakaba dokar hana fita

Rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto ta tabbatar da kafa dokar hana fita a karamar hukumar Sabon Birni a jihar, bayan da matasa suka tayar da tarzoma kan kashe sarkin Gobir, Isa Muhammad Bawa.
Kakakin rundunar, ASP Ahmed Rufa’i, ya ce ba za a yarda da wani motsi a yankin daga karfe 6 na safe zuwa karfe 6 na yamma ba har sai an samu sanarwar da ta sauya hakan.
Ya ce an dauki wannan matakin ne don dawo da doka da oda a yankin.
Daruruwan matasa sun cika wasu manyan hanyoyin yankin tare da kunna wuta a manyan tituna.
 An kuma ce matasan sun banka wa sakatariyar jam’iyyar APC ta karamar hukumar wuta tare da kone wata kotu.
Haka kuma sun balle wani rumbun ajiya na gwamnati na karamar hukumar inda suka lalata takin zamani.

Manoman citta a Nijeriya sun yi asarar Naira biliyan 12 a shekarar 2023 – Minista Noma

 

Gwamnatin tarayya ta ce manoman citta a Nijeriya sun yi asara da ta kai Naira biliyan 12 sakamakon wata annobar da ta lalata amfanin gonakin su a shekarar 2023.

Karamin ministan noma da samar da abinci, Aliyu Abdullahi ne ya bayyana haka a wajen taron Inshorar aikin gona a Abuja.

Ministan ya ce manoman sun yi asarar sama da kashi 90 cikin 100 na yawan amfanin gonakin da suke noma a kakar bara.

EFCC ta musanta raba kudaden da ta kwace hannun Emefiele

0

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta musanta rahotannin da ke cewa jami’anta sun raba wasu kadarorin da aka kwato daga tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele da mukarrabansa.

A wata sanarwa da kakakin hukumar, Dele Oyewale, ya fitar a ranar Laraba, ya musanta rade-radin da ake ya dawa a kafar sada zumunta ta zamani.

Hukumar ta ce wata jaridar yanar gizo ce mai suna Sahara Reporters ta wallafa, inda ta yi zargin cewa N54bn tayi batan dabo tsakanin wasu ministoci da mataimakan Shugaba Tinubu tare da hadin gwiwar jami’an EFCC.

Tanko Yakasai ya nisanta kansa daga rade-radin kafa jam’iyyar Arewa

Tsohon mashawarci na musamman ga marigayi shugaban kasa Shehu Shagari, Tanko Yakasai, ya nesanta kansa daga wani labari da jaridar Punch ta yanar gizo ta wallafa na kafa wata sabuwar kungiyar siyasa mai suna “The League of Northern Democrats.”

A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar 21 ga Agusta, 2024, aka bai wa manema labarai a Kano.

Yakasai ya kara da cewa “Tun da farko ban yi niyyar yin magana game da wannan lamarin ba.”

“ina kira ga jama’a da su yi watsi da rahoton da jaridar Punch Online Media ta bayar, domin ba ni da hannu a cikin masu shirya taron ko kuma kungiyar da ake magana a kai.”

Ina nan cikin PDP zan ci gaba da zama – Wike

0

 

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce ba zai fice daga jam’iyyar PDP ba duk da rikicin cikin gida da ake fama da shi.
Ya yi wannan jawabi ne a ranar Laraba a yayin wani taron manema labarai domin cika shekara guda a kan mukamin sa.
Matakin na Wike ya zo ne a daidai lokacin da ake gwabza fada na neman mulkin jam’iyyar PDP reshen jihar Ribas.

Ban taba nada Bashir Hadejia mukami ba, in ji Gwamnan jihar Zamfara, Dauda

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawan ya sanar cewa bai taba nada Bashir Hadejia wani mukami a cikin gwamnatisa ba kamar yadda ake yadawa.
Gwamna Dauda na magana ne a cikin shirin “One-on-One na gidan Talabijin na Channels, inda ya ce ko wasikar da ke yawo kan wannan batun, ba ta gaskiya ba ce, ba ta da tushe bare makama.
Gwamnan ya cigaba yana cewa a duk lokacin da zai nada wani mukami a gwamnatinsa, yana sanar da kafafen yada labarai.
“Na kalubalanci cewa ko ma wanene da ya fito ya nuna inda muka sanar da nada Bashir Hadejia.” In ji Gwamnan Dauda Lawan.
Ya ce a saman faifai suke tafiyar da gwamnatinsu a jihar, babu wani nuku-nuku, illa siyasa ce kawai ‘yan adawa ke neman yin amfani da ita domin shafa masa kashin kaji.