DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Saturday, April 11, 2026
Home Blog Page 425

Sama da gidaje dubu 9,733 suka zube sakamakon guguwar iska a Adamawa – NEMA

Sama da gidaje dubu 9,733 suka zube sakamakon guguwar iska a Adamawa – NEMA
Sama da gidaje 9,733 ne guguwar iska ta shafa a jihar Adamawa a shekarar 2024, kamar yadda hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa NEMA ta bayyana.
Shugaban sashin ayyuka na musamman a hukumar ta NEMA a Adamawa, Ladan Ayuba ya bayyana haka a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN a Yola.
Ya ce hukumar ta gudanar da tantancewar a kananan hukumomin da abin ya shafa da suka hada da, Jada, Hong, Mayo-Belwa, Madagali da Fufore.
Ayuba ya kuma bukaci mazauna yankunan da ambaliyar ta afku da su kaura zuwa wurare mafi aminci ko mafi tsayi domin kare lafiyarsu.
Ya ce gargadin ya zama wajibi ne saboda hasashen Nimet cewa Adamawa na cikin jihohin da za su fuskanci ambaliyar ruwa a shekarar 2024.
Jami’in hukumar ta NEMA ya kuma shawarci mazauna yankin da su rungumi dabi’ar sauraron rediyo don samun bayanai masu dacewa da kuma bin umarnin hukumar.

Sabon Fira Ministan Birtaniya Starmer ya yi taron majalisar ministoci na farko

Sabon Fira Ministan Birtaniya Starmer ya yi taron majalisar ministoci na farko

Fira Minista Keir Starmer ya gudanar da taron majalisar ministocinsa na farko bayan samun nasara da yayi a zaben da ya tabbatar dashi a matsayin sabon Fira Ministan Birtaniya

Starmer ya yi maraba da sabbin ministocin, yana mai cewa muna da ayyuka da yawa da za mu yi, don haka yanzu zamu ci gaba da aikinmu.

Daga cikin matsalolin da suke fuskanta sun hada da bunkasa tattalin arzikin kasa mai durkushewa, gyara tsarin kiwon lafiya.

Wani farfesa, a fannin siyasa a Jami’ar Queen Mary ta Landan Tim Bale, ya ce saboda jam’iyyar Labour ta samu gagarumin rinjaye ba ya nufin cewa duk matsalolin da gwamnatin Conservative ta fuskanta sun tafi.

Nijar, Mali da Burkina Faso ba za su koma kungiyar ECOWAS ba – Janar Tiani na Nijar

Nijar, Mali da Burkina Faso ba za su koma kungiyar ECOWAS ba – Janar Tiani na Nijar

Shugaban mulkin sojan Jamhuriyar Nijar, Janar Abdourahamane Tiani, ya bayyana cewa, al’ummar kasarsa, tare da makwabciyarta Mali da Burkina Faso, sun juya wa kungiyar ECOWAS baya.

Ya bayyana hakan ne a yayin bude taro dake gudana a birnin Yamai tsakanin kasashen yankin Sahel uku da suka fice daga babbar kungiyar a farkon wannan shekarar.

Shugaban hukumar ta ECOWAS, Dr Omar Alieu Touray, a ranar Alhamis din da ta gabata, ya koka da cewa, duk da kokarin da kungiyar kasashen yankin ke yi na dawo da kasashen Mali, Burkina Faso da Nijar, amma kasashen uku ba su nuna wata alamar dawowa ba.

A yayin da yake jawabi a wajen bude taro karo na 92 ​​na majalisar ministocin kungiyar a Abuja, ya ce har yanzu kungiyar ECOWAS ba ta kafa tsarin tattaunawa da mahukuntan kasashen Sahel din uku kan matakin da suka dauka na janye mambobinsu daga kungiyar ba.

A ranar 28 ga watan Junairun da ya gabata ne dai mahukuntan kasashen Burkina Faso da Mali da Nijar suka sanar da ficewa daga kungiyar ta ECOWAS.

KEDCO ta mayar da lantarkin jami’ar Aliko Dangote bayan biyan wani kaso na tarin bashin da ake bin jami’ar

KEDCO ta mayar da lantarkin jami’ar Aliko Dangote bayan biyan wani kaso na tarin bashin da ake bin jami’ar 

Kamfanin Rarraba wutar lantarki ta Kano, KEDCO, ya maida wutar lantarki a jami’ar kimiyya da fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil, bayan biyan Naira miliyan 100.

Mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Musa Yakasai, ya tabbatar da maido da wutar lantarki ga kamfanin dillancin labaran Nijeriya a wata tattaunawa ta wayar tarho a ranar Juma’a.

Ya ce an dawo da wutar lantarki a cibiyar da misalin karfe 4 na yamma bayan an biya kusan Naira miliyan 100.

An katse wutar jami’ar ne sakamakon bashin Naira miliyan 248 da kamfanin na KEDCO ke bin jami’ar.

Kamfanin ya dauki matakin ne duk da biyan Naira miliyan 20 daga cikin Naira miliyan 60 da jami’ar ta jihar ke biyan duk wata.

Mista Yakasai ya alakanta hakan ne da tsoma bakin gwamnatin jihar Kano da gidauniyar Dangote, inda suka fara biyan Naira miliyan 100 ga KEDCO.

Gwamnatin jihar ta kuduri aniyar daidaita wasu basussuka, yayin da gidauniyar Dangote ta binciko mafita mai dorewa kamar kananan grid masu amfani da hasken rana.

Hukumar gudanarwar jami’ar ta nuna godiya ga duk wanda aka samu da hannu tare da bukaci jami’ar

Sarkin musulmi ya bayyana ranar Lahadi a matsayin ranar sabuwar shekarar Musulunci ta 1446 bayan hijira

Sarkin musulmi ya bayyana ranar Lahadi a matsayin ranar sabuwar shekarar Musulunci ta 1446 bayan hijira

Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci, Muhammad Sa’ad Abubakar, ya ayyana ranar Lahadi 7 ga Yuli, 2024, a matsayin ranar farko ga watan Muharram, a daidai lokacin da aka shiga shekarar Musulunci ta 1446 bayan Hijira.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin ba da shawara kan harkokin addini na majalisar Sarkin Musulmi, Sambo Junaidu, a ranar ya fitar a ranar juma’a.

Ya bayyana cewa babu wani rahoton ganin watan da kwamitocin ganin wata na kasa da suka samu a fadin kasar.

Sanarwar ta ce, Kwamitocin ganin wata na kasa daban-daban a fadin kasar nan ba su samu rahoton ganin jinjirin watan Al-Muharram ba a ranar juma’a wato 29 ga watan Zulhijja shekara ta 1445 bayan hijira. Asabar 6 ga Yuli, ita ce 30 ga Zulhijja.

Sarkin Musulmi ya taya musulman Nijeriya murnar shiga sabuwar shekara,ya bukace su da su ci gaba da yi wa Nijeriya addu’o’in zaman lafiya da ci gaba.

‘Yan Nijeriya miliyan 82 na iya fuskantar yunwa nan ba da jimawa ba, in ji MDD

 ‘Yan Nijeriya miliyan 82 na iya fuskantar yunwa nan ba da jimawa ba, in ji MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta yi hasashen cewa ‘yan Nijeriya miliyan 82, kusan kashi 64 cikin 100 na al’ummar kasar za su iya fama da yunwa nan da shekara ta 2030, inda ta yi kira ga gwamnati da ta magance matsalolin da kasar ke fuskanta.

Hasashen ya zo ne sakamakon hauhawar farashin kayan abinci da ake ci gaba da yi a kasar.

A cewar hukumar kididdiga ta kasa, hauhawar farashin kayan abinci a Nijeriya ya kai sama da kashi 40.66 cikin 100 a watan Mayun 2024, wanda ya zarce na watan da ya gabata.

A shekarar 2023, hukumar abinci da aikin noma ta yi hasashen cewa akalla ‘yan Nijeriya miliyan 2.6 a jihohin Borno, Sokoto da Zamfara, da kuma Abuja na iya fuskantar matsalar abinci tsakanin watan Yuni zuwa Agusta 2024.

Ya kamata masu zuba jari a Nijeriya su fadada tunanin su- Kashim Shettima

Ya kamata masu zuba jari a Nijeriya su fadada tunanin su- Kashim Shettima 
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya yi kira ga masu zuba jari a kasar da su binciki abubuwa da dama na albarka tun kasa da  Nijeriya ke da su wadanda ba man fetur ba, inda ya ce akwai dimbin alheri a ciki
Ya bayyana aikin noma, masana’antu, makamashin da ake iya sabuntawa da kuma fasahar zamani, a sauran bangarori a matsayin hanyoyin zuba jari da za a iya ganowa, yana mai cewa sun yi daidai da abubuwan da gwamnatin su ta sa a gaba na ci gaban kasa da aka zayyana a cikin shirin farfado da tattalin arziki da ci gaban Nijeriya.
Shettima, wanda ya bayyana hakan a ranar Juma’a a yayin taron masu saka hannun jari na kasashen waje a fadar shugaban kasa, Abuja, ya bayyana cewa, ajandar abubuwa takwas na gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yana nuna hanyoyi daban-daban na saka hannun jari, daga noma zuwa makamashi.
A cewar wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da yada labarai, Stanley Nkwocha, ya fitar, Shettima ya ce, ta hanyar karfafa gwiwa da hadin gwiwar jama’a, muna da burin bullowa da abubuwan da za a iya samu a wadannan sassan. inganta samar da ayyukan yi da karfafa zamantakewa da tattalin arziki a fadin Nijeriya.

Kotu ta saka ranar da Ganduje zai san makomarsa a shugabancin APC

Kotun tarayya a Abuja ta saka 18 ga watan Satumbar, 2024 a matsayin ranar da za ta yanke hukunci kan taƙaddamar shugabancin jam’iyyar APC ta kasa da Abdullahi Ganduje ke jagoranta.
Hon Abdullahi Saleh Zazzaga, jagoran kungiyoyin jam’iyyar APC na yankin arewa ta tsakiyar Nijeriya ne dai ya jagoranci mutanensa, suka garzaya kotu neman sai Abdullahi Ganduje ya sauka daga shugabancin jam’iyyar APC.
‘Yan yankin Arewa ta tsakiyar dai na cewa kundin tsarin mulkin jam’iyyar ne ya ba su damar a ba su shugabancin jam’iyyar tun da wanda ya sauka daga bangarensu yake, kuma ba wa’adin mulkinsa a kare ba.
Alkalin kotun tarayyar Mai Shari’a Inyang Ekwo ya saka 18 ga watan Satumba na wannan shekarar domin yanke hukunci a kan wannan sa-toka-sa-katsi.

Rundunar sojojin Nijar ta hallaka ‘yan ta’adda sama da 100 a sabon farmaki

https://drive.google.com/uc?export=view&id=1wxxPQ8U769PsvIhqS5Hj3jv-T7F1CLG7
A cikin wata sanarwa da ta fitar a wannan rana ta Alhamis, rundunar sojojin Nijar din ta sanar da samun nasarar kashe ‘yan ta’adda sama da 100 a yayin wani farmakin ramuwar gayya da ta kai  ta sama da kasa a kan wadanda take zargi da kisan sojojin kasar 20 a yankin Tassia da ke cikin karamar hukumar Téra na jihar Tillaberi a ranar 25 ga watan Yunin da ya gabata
Kazalika sanarwar rundunar tsaron kasar ta ce daga ranar daya zuwa uku ga watan nan wani samame da ta kai a cikin kasuwannin Dougouro da Bankilare dukkan su cikin karamar hukumar ta Téra ya bata damar hallaka ‘yan ta’adda 8 da kuma kama wasu 19 
A dabra guda kuma rundunar ta ce a ranar daya ga watan dai na Yulin nan da muke ciki ta yi nasarar kashe wasu ‘yan ta’addar 20 tare da ragargaza kayan aikinsu a yayin wani barin wuta da ta musu a maboyarsu ta sama da ke da nisan kusan kilomita 4 daga arewa da Kokoloko da ke kan iyaka da Burkina Faso

Makonni uku a jere buhun Masara ya gaza sakkowa daga naira 100,000

Buhun masara ya fi tsada a kasuwar Mile 12 International Market jihar Legos da ke kudancin Najeriya, ana sayar da buhunta kan kuɗi N105,000, inda a makon da ya shude aka saya N100,000.

Ita kuwa kasuwar Mai’adua jihar Katsina farashin dai bai gusa ba daga na makonni biyu da suka gabata da aka saya N95,000.
Sai dai a kasuwar Karamar Hukumar Gombi a jihar Adamawa masarar ta sauka a jiya, inda aka sayar da buhun masarar N90-95000, bayan da a makon jiya aka sayar N100-102,000
An samu sauƙin N7000 a mako guda.
 
N90,000 cif aka sayi buhun masara a kasuwar Giwa jihar Kaduna a makon nan, bayan da a makon jiya aka saya N88,000.
A kasuwar Dandume jihar Katsina an sayi buhun masara mai cin tiya 40 N87,000-90,000 a satin nan, amma a makon da ya wuce N85,000-88,000 aka sayar da buhun masara a kasuwar.
Sai kuma kasuwar Dawanau jihar Kano,an sayi buhun masara N87,000 a makon farko na watan Yulin shekarar 2024, yayin da makon jiya aka sayar N85,000 nan ma an samu ragin 2000 cif.
Ita kuwa Shinkafar Hausa na ci gaba da sauka a kasuwar Mai’adua jihar Katsina wanda ake sayar da buhunta N140,000 a wannan satin, amma a satin da ya kare N145,000 ake sayar da buhun shinkafa ‘yar gida.
Sai dai farashin shinkafar ya bambanta da na kasuwar Dandume a jihar Katsinan, inda aka sayar da buhun N157-160,000 a makon nan, amma a makon da ya gabata N140-170,000 ake sayar da buhun,ya dai danganta da kyan Shinkafar.
A kasuwar Dawanau jihar Kano an sayi buhunta N150,000 a satin nan, yayin da a makon jiya aka saya N155,000, an samu sauƙin 5000 kenan a wannan mako.
Shinkafar dai na ci gaba da sauka a sassan kasuwannin kasar nan, N150,000 cif aka sayar da buhun shinkafar Hausa a kasuwar Dawanau da ke jihar a wannan mako, bayan da a makon jiya aka saya N155,000.
Sai dai a jihohin Adamawa da Legos N160,000 aka sayar da buhun shinkafar a makon nan, bayan da a makon da ya gabata aka saya N150,000 a Karamar Hukumar Girie a jihar Adamawa.
Shinkafar Bature kuwa ta fi tsada a kasuwar Dawanau jihar Kano da aka saya N90,000 daidai a satin nan, yayin da a satin da ya shuɗe aka sayar N87,000.
To a kasuwar Giwa jihar Kaduna N88,000 aka sayi buhun Shinkafar Bature a wannan satin, farashin dai bai sauya da na makon jiya.
N82,000 ake sai da buhun shinkafar waje a kasuwar Mai’adua jihar Katsina a wannan makon, inda a makon jiya aka sai da N81,500.
A jihar Legas da ke kudancin Najeriya N80,000 ake sai da Buhunta a makon nan,haka farashin yake a makon jiya.
Sai kuma kasuwar Zamani da ke jihar Adamawa aka N78,000 a satin nan da ke dab da ƙarewa, amma a makon da ya gabata N67,500 kuɗin buhun Shinkafar waje yake a kasuwar.
Ga ma’abota cin alala da kosai sai in ce ku gyara zama don jin yadda farashin wake yake a wasu daga cikin kasuwannin kasar.
Farashin farin wake dai bai sauya tufafi ba da na makon jiya da aka saya N250,000 a kasuwar Mile 12 International Market da ke jihar Legas.
Haka zalika farashin waken bai canza daga na makon da ya gabata da aka sai da N165-170,000 a kasuwar Gombi a jihar Adamawa. 
Sai kasuwar Dandume jihar Katsina aka saya N190-194,000 a satin nan, yayin da a makon da ya gabata aka sayar kan kuɗi N180-190,000 a kasuwar.
Ita kuwa Kasuwar Giwa jihar Kaduna N180,000 ake sayar da Buhunta a wannan makon, amma a makon Jiya N175,000 kuɗin buhun fari wake.
A Kasuwar Dawanau jihar Kano N170,000 ake sayar da buhun farin wake a wannan makon, yayin da a makon da ya shude aka N178,000, an samu canjin N8000 kenan a mako guda.
N175-180,000 ake sai da buhun wake a kasuwar Mai’adua jihar Katsina, amma a makon jiya N175,000 ake sayar da buhunta.
Kwalin taliya ma ya fi tsada a kasuwar Mile 12 International Market da ke jihar da ake saidawa N18,000 a satin nan, inda a satin da ya gabata aka saida kan kudi N17,000 .
A kasuwar Dawanau jihar Kano an sayi kwalinta N16,000 cif a makon nan, yayin da a makon jiya aka saya N13,700. Karin N2300 kenan a mako ɗaya .
Sai kuma kasuwar Zamani da ke jihar Adamawa farashin kwalin taliya ya tashi a makon nan,wanda aka saya N16,000,sai dai a makon daya gabata N13,000. Ake sayar wannan ma an samu karin N3000 a sati guda.
A Mai’adua jihar Katsina da kasuwar Dandume a jihar N15,500 ake sayar da kwalin taliyar a makon nan.
To bari mu karkare farashin kayan abinci na makon nan da farashin kwalin taliya a kasuwar Giwa jihar Kaduna,an sayi kwalinta N15,000 daidai a makon nan, yayin da a makon jiya aka sayar N14,000 cif.
Alkaluman da hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ta fitar a watan Mayun shekarar 2024, ya nuna cewa farashin kayakin abinci ya haura da kashi 33.90%.
DCL Hausa A’isha Usman Gebi