Friday, April 10, 2026
Home Blog Page 438

Sojoji na zafafa hare-hare kan ‘yan bindiga a jihar Zamfara

Gwamna Dauda Lawal ya yaba wa rundunar hadin guiwa kan sabbin hare-haren matsin lamba kan ‘yan bindiga a jihar Zamfara.
A karshen makon da ya gabata ne rundunar soji ta kara tura wasu dakarun sojoji zuwa Zamfara a kokarin da suke yi na dakile ayyukan ‘yan bindiga a yankunan da ke fama da rikici a jihar.
A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana aikin samar da tsaro da sojoji ke ci gaba da yi a matsayin matakin da ya dace na dakile ayyukan ‘yan bindiga a Zamfara.
Sanarwar ta kuma jajanta wa al’ummomin da hare-haren ‘yan bindiga ya shafa a baya-bayan nan, tare da ba da tabbacin ci gaba da goyon bayan gwamnatin jihar ga sojojin da ke fagen daga.
Sanarwar ta kara da cewa: “Ayyukan da sojoji ke ci gaba da yi a yankunan da ke fama da karancin tsaro a Zamfara abin yabawa ne matuka, musamman idan aka yi la’akari da nasarorin da aka samu tun fara kai hare-hare a karshen makon da ya gabata.
“Aikin ya haifar da gagarumar nasara a kananan hukumomin Bungudu, Tsafe, Maru, da Zurmi, wanda ya yi sanadiyyar kisan jagoran ‘yan bindiga, Abu Dan Dunkwuifa, wanda ya shahara da ta’addanci a kauyukan Bungudu da Maru.
“A Magama Mai Rake da ke yankin Dansadau a karamar hukumar Maru, sojojin sun yi nasarar kashe ‘yan bindiga da dama.
“Harin da sojoji suka sake kai wa a Nasarawar Burkullu a karamar hukumar Bukkuyum ya yi sanadiyar ceto mutane da dama da aka yi garkuwa da su a kauyukan Kamaru, Tungar Rogo, da Matsare, tare da kwato shanu da dama da aka sace.
“Jita-jitar cewa an yi garkuwa da mutane sama da 500 ba gaskiya ba ne kuma wasu mutane ne da ba sa son zaman lafiya ya dawo a jihar Zamfara.
Gwamnan ya kuma jajanta wa al’ummar da ‘yan bindiga suka kai wa hari a jihar.
“Gwamnatin jihar Zamfara na son nuna juyayi ga al’ummomin da ‘yan bindiga suka kai wa hari kwanan nan. Mun himmatu sosai wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.
“Gwamnatinmu za ta ci gaba da tallafa wa sojojin da ke yaki da rashin tsaro tare da bayar da duk wani tallafin gaggawa ga wadanda rikicin ‘yan bindiga ya shafa a jihar.”

‘Yan Nijeriya milyan 4.8 na iya fama da karancin abinci a ban in ji majalisar dinkin duniya

Majalisar Dinkin Duniya UN ta yi hasashen cewa da yiwuwar mutane milyan 4.8 a Nijeriya su yi fama da matsanancin karancin abinci a shekarar nan ta 2024.
Bugu da kari, majalisar dinkin duniyar ta ce a kwai yara kanana milyan 5.9 a Nijeriya da ke fama da matsanancin karancin abinci.
Adadin kamar yadda Mohammed Fall, babban mai kula da ayyukan majalisar a Nijeriya ya ce, shi ne mafi girma a duk fadin duniya.
Ya ce akwai yara kanana ‘yan kasa da shekaru 5 su 700,000 da ke fama da karancin abinci da kuma wanda bai gina jiki a jihohin Borno, Adamawa da Yobe.

Hisbah ta kama ɗan jarida a Katsina

Hukumar Hisbah a jihar Katsina ta kama ɗan jarida Jamilu Mabai, wakilin gidan talabijin na Trust Tv a jihar Katsina.

Rahotannin da DCL Hausa ta samu sun nuna cewa hukumar ta Hisbah ta nemi dan jaridar ruwa a jallo sakamakon wani rubutu da ya yi a kafar sadarwa ta Facebook, wanda yake da alaƙa da zargin cin mutuncin hukumar da shugabanta

An kama Mabai ne a wannan Talata bayan da ya je hukumar da niyyar haɗa rahoto na zargin da ake ma hukumar na harbe wani dattijo mai sana’ar faci da bindiga, wanda hakan ake zargin ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Ƙungiyar FPL ta yi barazanar kai hare-hare a wasu wuraren hakar man fetur a Nijar

Sabuwar kungiyar tawayen nan ta Nijar Front Patriote de Libération (FPL) ta yi barazanar fara kaddamar da hare hare a wasu wuraren hakar man fetur a ƙasar 
A cikin wata sanarwa ce da ta fitar mai dauke da sa hannun shugaban ta a ranar 13 ga watan Mayun nan, sabuwar kungiyar tawayen ta bayyana cewa bayan cikar wa’adin mako gudan da ta bada na soke yarjejeniyar bashin kudi nan har milyan 400 na dalar Amurka da kasar China ta ba hukumomin mulkin sojan Nijar ba tare da an soke ba ta yi kira ga ‘yan Nijar da ma ‘yan kasashen ketare wadanda ba su ji ba su gani ba da su gaggauta barin wuraren da ake haka da sarrafa man fetur 
Kungiyar ta zana wasu wuraren da ta ce daga yanzu su ne wuraren da za ta fara kaddamar da ayyukan ta
Cikin wuraren da kungiyar ta zano har da kamfanin matatar mai ta SORAZ da ke jihar Damagaram da dukkan wasu wuraren hako man na Agadem da ke cikin jihar Diffa
Kungiyar ta ce za ta janye daga wannan matsaya ta ta ne kawai idan har an maido kasar ta farkin dimokaradiyya da kundun tsarin mulkin
Kungiyar ta FPL ta ce manufarta shi ne ta hana satar man fetur din Nijar da wasu tsiraru suke yi don arzuta danginsu tare saka al’ummar kasar cikin mawuyacin hali
A karshe kungiyar ta ce ta shirya kirkiro hanyoyin da za su bada damar rabon arzikin man fetur cikin adalci domin gudanar da ayyukan masu muhummanci don amfanin al’ummar Nijar

Mahamadou Issoufou ya maka tsohon jakadan Faransa a Nijar kotu

Mahamadou Issoufou

Tsohon shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou ya maka tsohon jakadan Faransa a Nijar Sylvain Itté a gaban kotu bisa zarginsa da bata masa suna

Tsohon jakadan Faransa dai a Nijar ya zargi tsohon shugaban kasar Issoufou Mahamadou da hannu a cikin juyin mulkin ranar 26 ga watan Yulin bara da ya yi awan gaba da kujerar aminin sa Bazoum Mohamed

Tsohon shugaban kasar ya shigar da wannan kara ne a gaban babban kotun birnin Yamai

Shugaba Tinubu ya kaddamar da gangamin sanya yara kanana makarantun boko

Shugaban kasa Bola Tinubu ya kaddamar da wani kamfen na inganta ilimi da bunkasar fasaha da daidaiton jinsi.

Gangamin da aka yi wa lakabi da, “duk daya muke” wato #WeAreEqual, wani shiri ne na kungiyar matan shugabannin kasashen Afirka OAFLAD.

An kaddamar da gangamin a kasashen Nahiyar Afirka 15 a fannoni daban-daban, inda aka mai da hankali kan kiwon lafiya, ilimi, karfafa tattalin arziki, da yaki da cin zarafin mata.

Da yake jawabi a wajen kaddamar da gangamin da aka gudanar a fadar shugaban kasa, Shugaba Tinubu ya jinjina wa kudurin matan shugabannin kasashen Afirka, a matsayinsu na mambobin kungiyar OAFLAD, na inganta daidaiton jinsi tare da takaita bambancin jinsi a fadin nahiyar.

IHR na rokon da a tsaurara tsaro a sasanonin maniyyata aikin hajjin Nijeriya

Kungiyar nan mai zaman kanta da ke ba da rahotannin yadda aikin hajji da Umrah ke gudana wato Independent Hajj Reporters, ta yi kira ga gwamnatin tarayyar Nijeriya da ta jihohi da su samar da wadataccen tsaro ga maniyyatan aikin hajjin bana na 2024.
Kiran wannan kungiya na a cikin wata sanarwa daga shugabanta Alhaji Ibrahim Muhammad da DCL Hausa ta samu kwafi, wanda kiran ya zo daidai da lokacin da ake dab da fara jigilar mahajjatan Nijeriya zuwa kasar Saudiyya don sauke farali.
Sanarwar ta ce akwai sama da maniyyatan Nijeriya 65,000 da za su rika barin gidajensu zuwa sansanonin alhazai daban-daban domin tantance su da kuma jigilarsu zuwa filayen jirage kusan 15 cikin kwanaki 30 masu zuwa, don haka ne kungiyar ke kira da babbar murya ga hukumomi na su saka idanu sosai don tabbatar da tsaron rayukan al’umma.
Da kungiyar ta yaba da irin kokarin da hukumomin tsaro suka yi a ayyukan hajji na baya, yanzu haka ma kungiyar ba ta yi kasa a guiwa ba wajen sake tunasar da gwamnatin tarayya da ta jihohi da su sanya jami’an tsaro na musamman da z asu rika sintiri don kare rayukan maniyyatan.
Alhaji Ibrahim Muhammad a cikin sanarwar ya kuma shawarci hukumomin kula da aikin hajji na jihohi da su gargadi maniyyatansu da kada su rika zuwa sansanonin alhazai da tawagar ‘yan rakiya da yawa.

An kara kudin haya a Abuja, mazauna na ta guna-guni

Rahotannin da DCL Hausa ta samu daga jaridar Daily Trust sun ce an samu karin daga gidan da ake biyan N600,000 yanzu an mayar N850,000 a shekara.

Bayanai dai sun ce yanzu haka mazauna birnin tarayyar na ta guna-gunin wannan karin kudin da aka yi musu.
Kazalika, akwai wanda ake biyan daki daya kan kudi N150,000 yanzu an mayar N250,000 a shekara a Unguwar Dei-Dei. Bugu da kari, akwai wani mazaunin yankin Dutse da ke biyan N550,000 a shekara dakuna biyu wato Two Bed Room, amma yanzu an mayar da kudin sun koma N7000,000.
A yankin Kuje kuwa, akwai gidan da ake biyan N200,000 a shekara, amma yanzu ya koma N280,000 har ma N350,000 a shekara ya danganta da inda gidan yake.
Sai dai da jaridar Daily Trust ta tuntubi masu gidajen hayar, sun shaida cewa matsim tattalin arzikin da Nijeriya ke ciki ne ya sanya su wannan karin, ba da son ransu ba.

Shugaba Tinubu ya taya murna ga sabon shugaban kasar Chad

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya taya zababben shugaban kasar Chad Mahamat Idris Deby murna bayan nasarar lashe zaben shugaban kasa da ya yi.
Shugaban na Nijeriya ya hakikance cewa yadda aka gudanar da sahihi kuma ingantaccen zabe a kasar, ya nuna karara yadda al’ummar kasar Chad ke son dimokradiyya ta dore yadda ya kamata.
A cikin wata sanarwa daga mai magana da yawun shugaban kasa Mr Ajuri Ngelale, ta ce Nijeriya za ta yi aiki kafada da kafada da kasar Chad ganin yadda kasashen biyu suke mayar da hankali wajen inganta tsaro da zaman lafiya.
Shugaban kasar ya yi kiran da a cigaba da hadin kai a tsakanin kasashen biyu, sannan ya yi addu’a ga sabon shugaban kasar da ya sauke nauyin al’umma da ke kansa.

NAHCON ta aike da ma‘aikatan farko da za su tarbi maniyyata zuwa Saudiyya

Tawagar ma’aikata 43 daga hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON za su tashi daga Abuja a gobe Lahadi, zuwa kasar Saudiyya, domin murnar tarbar jirgin farko na mahajjatan Nijeriya a kasar Saudiyya.
Tawagar da ta kunshi jami’an hukumar NAHCON 35 da ma’aikatan lafiya 8 za su je kasar Saudiyya domin shirin karshe na karbar mahajjatan Nijeriya daga jihar Kebbi da za su isa Saudiyya a ranar Laraba 15 ga watan Mayu domin gudanar da aikin Hajjin bana na shekarar 2024.
Da yake jawabi ga tawagar a wani dan takaitaccen biki na ban kwana da aka gudanar a dakin taro na hukumar, Abuja, shugaban hukumar Malam Jalal Ahmad Arabi ya gargadin cewa hukumar za ta dauki tsattsauran mataki a kan duk wanda aka samu rahoton ya kauce wa ka’idar aiki ga amanar da aka dora musu.