Sojoji na zafafa hare-hare kan ‘yan bindiga a jihar Zamfara
‘Yan Nijeriya milyan 4.8 na iya fama da karancin abinci a ban in ji majalisar dinkin duniya
Hisbah ta kama ɗan jarida a Katsina
Hukumar Hisbah a jihar Katsina ta kama ɗan jarida Jamilu Mabai, wakilin gidan talabijin na Trust Tv a jihar Katsina.
Rahotannin da DCL Hausa ta samu sun nuna cewa hukumar ta Hisbah ta nemi dan jaridar ruwa a jallo sakamakon wani rubutu da ya yi a kafar sadarwa ta Facebook, wanda yake da alaƙa da zargin cin mutuncin hukumar da shugabanta
An kama Mabai ne a wannan Talata bayan da ya je hukumar da niyyar haɗa rahoto na zargin da ake ma hukumar na harbe wani dattijo mai sana’ar faci da bindiga, wanda hakan ake zargin ya yi sanadiyyar mutuwarsa.
Ƙungiyar FPL ta yi barazanar kai hare-hare a wasu wuraren hakar man fetur a Nijar
Mahamadou Issoufou ya maka tsohon jakadan Faransa a Nijar kotu
![]() |
| Mahamadou Issoufou |
Tsohon shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou ya maka tsohon jakadan Faransa a Nijar Sylvain Itté a gaban kotu bisa zarginsa da bata masa suna
Tsohon jakadan Faransa dai a Nijar ya zargi tsohon shugaban kasar Issoufou Mahamadou da hannu a cikin juyin mulkin ranar 26 ga watan Yulin bara da ya yi awan gaba da kujerar aminin sa Bazoum Mohamed
Tsohon shugaban kasar ya shigar da wannan kara ne a gaban babban kotun birnin Yamai
IHR na rokon da a tsaurara tsaro a sasanonin maniyyata aikin hajjin Nijeriya
An kara kudin haya a Abuja, mazauna na ta guna-guni
Rahotannin da DCL Hausa ta samu daga jaridar Daily Trust sun ce an samu karin daga gidan da ake biyan N600,000 yanzu an mayar N850,000 a shekara.

.jpeg)
.jpeg)