Friday, April 10, 2026
Home Blog Page 440

Masara ta yi tsada a sassan jihar Lagos

Farashin kayan abinci na wannan makon a kasuwar Dawanau da ke jihar Kano, an saida buhun Masara N60,000 daidai a makon nan, bayan da makon da ya gabata aka sayar N58,000.
Masarar ta fi tsada a kasuwar Mile 12 International Market da ke jihar Legas, da aka saya N67,000, yayin da a makon da ya shude aka saya N65,000 an samu karin dubu 2000 kenan.
A kasuwar Mai’adua jihar Katsina, an sayar da buhun N64,000 a wannan satin, inda a makon da ya gabata aka sayar kan kuɗi N62,000.
Sai kasuwar Giwa da ke jihar Kaduna da aka sai da buhun masara kan kudi ₦59,000 a makon nan, amma a makon jiya N57,000 aka sai da buhun.
To a kasuwar Gombi da ke jihar Adamawa masarar ta ɗan sauka, an sayi buhun N56-58,000 a makon nan, bayan da a makon da ya wuce aka sayar N57-60,000 cif.
Masarar ta fi sauki a kasuwar Gombi da ke jihar Adamawa a arewa maso gabashin Nijeriya da aka saya N55,000 a makon da ke dab da ƙarewa, bayan da a makon da ya shude aka saida N57-60,000.
Idan muka je ga batun Shinkafar Hausa kuwa ta fi sauki a kasuwar Dawanau a da ke jihar Kano a makon nan, an sayi buhun Shinkafar Hausa N122,000, sai dai a makon jiya N118,000 aka sayar da buhun.
Sai dai fa, batun ya sha banban da kasuwar Mile 12 International Market Legos da aka sayar da buhun N142,000 a wannan makon, inda makon da ya gabata aka sayar N120,000 an samun karin kudi har N20,000 daidai a makon guda.
Sai kuma kasuwar Giwa da ke jihar Kaduna da ke biye mata, inda aka sayar da buhun shinkafar Hausa N125,000, amma a makon jiya N120,000 ake sai da buhun, an samu karin N5000 kenan a makon guda kacal.
Shinkafar ta ɗan haure a kasuwar Girie da ke jihar Adamawa a wannan makon, da aka sayar N130,000, sai dai a makon da ya gabata kuwa an sai da N110,000, an samu karin N20,000 kenan a makon nan.
To a kasuwar Kashere da ke karamar hukumar Akko a jihar Gombe kuwa kuɗin buhun Shinkafar Hausa bai sauya zani ba, inda aka sayi buhun N120-130,000, a makon da ya gabata, haka nan aka sai da a makon nan.
An sayi buhun Shinkafar Hausa N130,000 daidai a wannan makon, yayin da a makon jiya aka sayar N120,000 a kasuwar Mai’adua a jihar Katsina.
To a bangaren Shinkafar waje kuwa an sai da buhun kan kuɗi N75,000 a kasuwar Dawanau da ke jihar Kano a makon nan, inda a makon jiya aka sai da N71,000.
A Mai’adua jihar Katsina, an sayi buhun Shinkafar Bature N68-69,000 a wannan makon, yayin da a makon jiya aka saya N62,000, an samu karin N7000 kenan kan farashin makon jiya.
An sayi shinkafar Bature N71,000 a kasuwar Mile 12 International Market da ke jihar Legos a satin nan, yayin da a makon jiya aka sai da N65,000.
Ita ma dai kasuwar Kashere da ke jihar Gombe N75,000 ake sai da buhun a makon nan da ke shirin karewa, bayan da aka saya N65,000 a makon da ya gabata, hakan ke nuni da cewa an samu karin N10,000 kenan a mako ɗaya .
N73,000 aka sayi buhun Shinkafa ‘yar waje a kasuwar Zamani da ke jihar Adamawa a satin nan, inda a makon da ya shude aka saya N55,000.
To bari ƙarƙare farashin shinkafar na wannan makon da kasuwar Giwa na jihar Kaduna, an sayar da buhun shinkafar waje N68,000 a satin nan, amma a satin da da ya wuce N65,000 ake sai da buhun.
Ga ma’abota cin alala da kosai kuwa, wake fari ya fi tsada a kasuwar Mile 12 International Market da ke jihar Legos, da aka sai da N130,000 
Sai kasuwar Dawanau a jihar Kano a arewacin kasar, inda aka sayar da buhun N113-120,000 a kasuwar.
A Mai’adua jihar Katsina kuwa, an sayi buhun farin waken N117,000 a makon nan.
Da DCL HAUSA ta yi tattaki zuwa kasuwannin jihohin Gombe da Kaduna, ta taras da cewa ana sayen buhun farin waken kan kudi N107,0000 a kasuwar Giwa ta jihar Kaduna da kuma kasuwar Kashere da ke jihar Gombe.
Sai dai waken ya fi sauki a kasuwar Gombi da ke jihar Adamawa a wannan makon da aka sayar N90-95,000.
Bari mu kammala Farashin kayakin abinci na satin nan da farashin Kwalin taliyar Spaghetti.
A wannan makon da ke mana ban kwana dai, taliyar ta fi tsada a kasuwar Mai’adua jihar Katsina da sayar da kwalin N14,500, bayan da makon da ya shude aka saya N13,700.
Haka nan a wannan makon ma kudin kwalin taliyar N14,000 ne a kasuwannin jihohin Gombe da Kaduna, hakan kuwa aka sai da a makon da ya gabata ma.
A kasuwar Zamani da ke jihar Adamawa an sayi kwalin taliyar N13,500 a makon nan, yayin da a makon jiya aka sai da kan kudi N13,000, cif cif.
N13,500 ake sai da kwalin taliya a kasuwar Mile 12 International Market da ke jihar Legas a makon nan, haka zancen yake a makon da ya gabata.
A kasuwar Dawanau da ke Jihar Kano N14,000 ake sayar da kwalin taliyar a makon da ya gabata, yayin da a wannan makon da ke dab da ƙarewa ake sayarwa kan kudi N13,000, an samu ragin N1000 guda kan farashin makon da ya gabata.
DCL HAUSA A’isha Usman Gebi.

Masara ta yi tsada a sassan jihar Lagos

Farashin kayan abinci na wannan makon a kasuwar Dawanau da ke jihar Kano, an saida buhun Masara N60,000 daidai a makon nan, bayan da makon da ya gabata aka sayar N58,000.
Masarar ta fi tsada a kasuwar Mile 12 International Market da ke jihar Legas, da aka saya N67,000, yayin da a makon da ya shude aka saya N65,000 an samu karin dubu 2000 kenan.
A kasuwar Mai’adua jihar Katsina, an sayar da buhun N64,000 a wannan satin, inda a makon da ya gabata aka sayar kan kuɗi N62,000.
Sai kasuwar Giwa da ke jihar Kaduna da aka sai da buhun masara kan kudi ₦59,000 a makon nan, amma a makon jiya N57,000 aka sai da buhun.
To a kasuwar Gombi da ke jihar Adamawa masarar ta ɗan sauka, an sayi buhun N56-58,000 a makon nan, bayan da a makon da ya wuce aka sayar N57-60,000 cif.
Masarar ta fi sauki a kasuwar Gombi da ke jihar Adamawa a arewa maso gabashin Nijeriya da aka saya N55,000 a makon da ke dab da ƙarewa, bayan da a makon da ya shude aka saida N57-60,000.
Idan muka je ga batun Shinkafar Hausa kuwa ta fi sauki a kasuwar Dawanau a da ke jihar Kano a makon nan, an sayi buhun Shinkafar Hausa N122,000, sai dai a makon jiya N118,000 aka sayar da buhun.
Sai dai fa, batun ya sha banban da kasuwar Mile 12 International Market Legos da aka sayar da buhun N142,000 a wannan makon, inda makon da ya gabata aka sayar N120,000 an samun karin kudi har N20,000 daidai a makon guda.
Sai kuma kasuwar Giwa da ke jihar Kaduna da ke biye mata, inda aka sayar da buhun shinkafar Hausa N125,000, amma a makon jiya N120,000 ake sai da buhun, an samu karin N5000 kenan a makon guda kacal.
Shinkafar ta ɗan haure a kasuwar Girie da ke jihar Adamawa a wannan makon, da aka sayar N130,000, sai dai a makon da ya gabata kuwa an sai da N110,000, an samu karin N20,000 kenan a makon nan.
To a kasuwar Kashere da ke karamar hukumar Akko a jihar Gombe kuwa kuɗin buhun Shinkafar Hausa bai sauya zani ba, inda aka sayi buhun N120-130,000, a makon da ya gabata, haka nan aka sai da a makon nan.
An sayi buhun Shinkafar Hausa N130,000 daidai a wannan makon, yayin da a makon jiya aka sayar N120,000 a kasuwar Mai’adua a jihar Katsina.
To a bangaren Shinkafar waje kuwa an sai da buhun kan kuɗi N75,000 a kasuwar Dawanau da ke jihar Kano a makon nan, inda a makon jiya aka sai da N71,000.
A Mai’adua jihar Katsina, an sayi buhun Shinkafar Bature N68-69,000 a wannan makon, yayin da a makon jiya aka saya N62,000, an samu karin N7000 kenan kan farashin makon jiya.
An sayi shinkafar Bature N71,000 a kasuwar Mile 12 International Market da ke jihar Legos a satin nan, yayin da a makon jiya aka sai da N65,000.
Ita ma dai kasuwar Kashere da ke jihar Gombe N75,000 ake sai da buhun a makon nan da ke shirin karewa, bayan da aka saya N65,000 a makon da ya gabata, hakan ke nuni da cewa an samu karin N10,000 kenan a mako ɗaya .
N73,000 aka sayi buhun Shinkafa ‘yar waje a kasuwar Zamani da ke jihar Adamawa a satin nan, inda a makon da ya shude aka saya N55,000.
To bari ƙarƙare farashin shinkafar na wannan makon da kasuwar Giwa na jihar Kaduna, an sayar da buhun shinkafar waje N68,000 a satin nan, amma a satin da da ya wuce N65,000 ake sai da buhun.
Ga ma’abota cin alala da kosai kuwa, wake fari ya fi tsada a kasuwar Mile 12 International Market da ke jihar Legos, da aka sai da N130,000 
Sai kasuwar Dawanau a jihar Kano a arewacin kasar, inda aka sayar da buhun N113-120,000 a kasuwar.
A Mai’adua jihar Katsina kuwa, an sayi buhun farin waken N117,000 a makon nan.
Da DCL HAUSA ta yi tattaki zuwa kasuwannin jihohin Gombe da Kaduna, ta taras da cewa ana sayen buhun farin waken kan kudi N107,0000 a kasuwar Giwa ta jihar Kaduna da kuma kasuwar Kashere da ke jihar Gombe.
Sai dai waken ya fi sauki a kasuwar Gombi da ke jihar Adamawa a wannan makon da aka sayar N90-95,000.
Bari mu kammala Farashin kayakin abinci na satin nan da farashin Kwalin taliyar Spaghetti.
A wannan makon da ke mana ban kwana dai, taliyar ta fi tsada a kasuwar Mai’adua jihar Katsina da sayar da kwalin N14,500, bayan da makon da ya shude aka saya N13,700.
Haka nan a wannan makon ma kudin kwalin taliyar N14,000 ne a kasuwannin jihohin Gombe da Kaduna, hakan kuwa aka sai da a makon da ya gabata ma.
A kasuwar Zamani da ke jihar Adamawa an sayi kwalin taliyar N13,500 a makon nan, yayin da a makon jiya aka sai da kan kudi N13,000, cif cif.
N13,500 ake sai da kwalin taliya a kasuwar Mile 12 International Market da ke jihar Legas a makon nan, haka zancen yake a makon da ya gabata.
A kasuwar Dawanau da ke Jihar Kano N14,000 ake sayar da kwalin taliyar a makon da ya gabata, yayin da a wannan makon da ke dab da ƙarewa ake sayarwa kan kudi N13,000, an samu ragin N1000 guda kan farashin makon da ya gabata.
DCL HAUSA A’isha Usman Gebi.

Gwamnatin kasar Benin ta hana lodar danyen man Nijar a ƙasar

Shugaban kasar Bénin Patrice Talon ya tabbatar wa duniya da matakin sa na hana lodar danyen man Nijar daga tashar jirgin ruwan kasar sa zuwa kasuwannin duniya

Shugaba Talon ya kuma nuna takaicinsa kan hawa dokin naki da hukumomin mulkin sojan Nijar suka yi na kin bude iyakar su da Bénin domin kuwa duk kokarin sa na neman samo masalaha a tsakanin kasashen biyu ya citura domin kasa samun gamsasshiyar amsa daga hukumomin na birnin Yamai sakamakon cewa har da ministan harkokin wajen shi ya tura wa mahukuntan na Yamai amma shiru

To amma ya ce a shirye yake ko a yanzu idan mahukuntan na Yamai suka amince suka bude iyakar su ya bar jiragen da suka zo domin daukar danyen man su dauka don ya ce yana fatan daidaituwar al’amura a tsakanin kasashen biyu aminan juna kuma ‘yan uwan juna

Marigayi Umaru Musa Yar’adua: Shi ake so ko halinsa….?

 Tunawa Marigayi Shugaba Ummaru Musa ‘Yar’adua  
Tun daga ranar 5th ga Watan Mayu na 2010,da Ajaliyar Malam Ummaru Musa ‘Yar’adua ta yi,tun daga jajibirin ranar wasu al’ummar Kasar nan ba tare da la’akari da bambamcin Bangare ko Yare ko Akida ko Siyasa ba, a Kasarnan baki daya sukan yi alhini don tunawa da Marigayi Shugaban Kasar Nijeriya Malam Ummaru Musa ‘Yar’adua.
 Wannan kuma bai rasa nasaba da ribarsa da aka ci a lokacin rayuwarsa da kuma jagoranci abin misali
Sai dai al’ummar Jahar Katsina ita zata fi karda dalilai dadama na tunawa da wannan Shugaba da ya rigayemu gidan gaskiya Shekaru <14> kenan a bana.

Yakubu Lawal

Musamman wasu Makusantansa na Siyasa suke jagorantar tarukan lakcha da na addu’o’in samun rahmar Ubangiji garesa
A wannan Shekarar abin da ya kara ankarar da al’umma a kan Marigayi Malam Ummaru Musa ‘Yar’adua ya cika Shekaru <14> da rasuwa shi ne taron manema labaru da wata Kungiya Mai suna Plesant Library and Book Club dake gaba-gaba wajen dabbaqa tarukan ta yi,tare kara fito da wasu batutuwa da za su iya amfanar duk mai muradin yin mulki a duniya,musamman a wannan lokaci da mafi rinjayen al’umma ke da bukatar kamanci ko madadi
An yi taron kamar yarda aka saba,tare da sa albarkar Shehunnan Malamai na Addini da na Siyasa da Shugabanni da Sarakuna da masu rike da Mukamai da dabam-dabam a matakai dabam-dabam. 
Gwamnan Jahar Katsina Mai ci yanzu mukarrabansa da Tsohon Gwamnan Jahar Katsina a shekaru <8> da suka gabata dama sauran wadanda suka maganta a bagiren sun yi tarayya a kan cewa Malam Ummaru Musa ‘Yar’adua Mutum ne MAI GUDUN DUNIYA DA YA SHINFIDA ADALCI NA SHUGABANCIN DA BAI DAMU DA ABIN DUNIYA BA,KUMA KOYI DA SHI MAFITA CE GA MAI SON YA FITA
Tabbas! Dukkan wadanda suka yi wannan shedar ga wannan Shugaba da ya kaura Shekaru <14> da suka shude,sun yi tarayya ce ta kut da kut da shi,musamman a lokacin da ya gwamnatanci Jahar Katsina daga 1999- 2007 da kuma gajeran lokacin da ya mulki Kasar nan ta Nijeriya. 
Bawai a tsakanin Shugabanni ba kadai, ko a bakin talakawan da Malam Ummaru ‘Yar’adua ya mulka,fatan dacewa a lahira suke masa,duk da Shekarun da ya zamaninsa, akwai shugabancin da aka ratso bayansa dadama.
Duk da cewar, a baya-bayan nan, a matakai na Jaha da Kasa, Malam Ummaru ‘Yar’adua shi ne Shugaba da ya rigayemu, ba a samu wanda ake fadin khairinsa ba zucci da baki kamarsa
Wannan ne ya sanya Maudu’in wannan rubutu ya karkata kan SHIN? SHI AKE SO KO HALINSA….?
Dalilin wannan Maudu’i shi ne Izma’in ra’ayoyi mabambamta sun nuna dole akwai dalili dayan-biyu da ya sa sunan Marigayi Shugaban bai kwaranye ba,kamar wasu na kafinsa da bayansa dama wasu dake raye,amman tauraronsu ya dishe koma ya bace kamar an yi khusufi.
Da ni da duk wanda ya bibiyi yarda taron addu’ar tunawa da wannan Shugaba ya gudana a wannan Shekarar zai lura da karuwar shigar masu fada-aji a fagen mulki da Siyasa dama masu tunanin nan, na kowar tuna bara bai ji dadin bana ba,ta fuskar canjin rayuwa.
Taken da aka yi wa Kundin da aka gabatar wato ‘Abinda ‘Yar’adua ya fada mani,kuma koyar dani’ wanda daya daga cikin yaransa na Siyasa a Katsina, Dr. Muttaqa Rabe Darma ya wallafa na bukatar duk wanda ya ci karo da wannan rubutu ya yi nazari kafin zagayowar irin wannan rana badi. 
Sannan mu tambaya kammu…
SHI muke So ko HALINSA ?
   Alkalamin:
 Yakubu Lawal
 Dan Jarida 
Jami’in Hulda da Jama’a

‘Yan sanda sun kama ‘yan fashi da makami da karin masu aikata laifuka daban-daban a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta ce ta yi nasarar kama mutane 22 da ake zargi da aikata fashi da makami da karin wasu mutane 36 da su ma ake zargi da aikata fyade da luwadi a jihar.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar ASP Aliyu Abubakar Sadiq a taron manema labarai a Katsina, inda ya fadi wasu nasarorin da rundunar ta samu a cikin watan Afrilu da ya gabata.
Kakakin rundunar ‘yan sandan ya ce sun kuma yi nasarar kama mutane 10 da ake zargi da hannu a wajen kisan kai. Sannan ya kara da cewa rundunar ‘yan sandan ta samu koke-koke 81 na aikata manyan laifuka da suka hada da kisan kai, fashi da makami, fyade da luwadi da satar shanu.
Ya ce cikin watan Afrilu da ya gabata, rundunar ‘yan sandan jihar ta yi nasarar kai koke-koke 49 a gaban kotu da aka kama mutane 145 da ake zargi da hannu cikin wadannan batutuwa.
Rundunar ‘yan sandan ta ce ta kuma yi nasarar hallaka mutane 12 da ake zargin ‘yan bindiga ne ta kuma ceto mutane 30 da aka sace ta kuma kwato dabbobi 492.
Kakakin rundunar ‘yan sandan ASP Aliyu Abubakar Sadiq ya ce a cikin wannan wata na Mayu kuwa, rundunar ‘yan sandan ta yi nasarar dakile wani yunkurin garkuwa da mutane da ‘yan bindiga suka tare wasu motocin haya biyu a kan hanyar Gusau-Funtua, inda ta ceto fasinjoji 52.

Tinubu zai dawo Najeriya bayan kwashe kwanaki a Turai

Fadar shugaban kasar Najeriya ta bayyana cewa shugaba Tinubu da mukarrabansa za su dawo Najeriya daga Turai a gobe Laraba.

Mashawarci na musamman kan bayanai da dabaru ga shugaban kasar Bayo Onanuga ne ya sanar a cikin wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X yau Talata.

Indai za’a iya tunawa a ranar 22 ga Afrilu, Shugaba Tinubu ya bar Abuja zuwa kasar Netherlands a wata ziyarar aiki da yakai.

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar tantance lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya rattaba hannu kan dokar tantance lafiyar masu son yin aure.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnatin, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce dokar na nufin daga yanzu babu wani aure da za a ɗaura shi a Kano ba tare da gabatar da sakamakon gwajin lafiya ba.

Hakan na nufin rage yiwuwar haihuwar yara masu wasu matsalolin kiwon lafiya kamar sikila, cutar kanjamau da ciwon hanta.

Jihar Katsina na duba yiwuwar fara daukar mata a kwalejinta ta horar da kwallo

Kwalejin horar da kwallon kafa ta jihar Katsina za ta fara daukar mata don horar da su kwallon kafa a Kwalejin don yin adalci ga kowane bangare.
Sai dai, Kwalejin kamar yadda gidan talabijin na Channels ya rawaito, hakan zai yiwu muddin dama ta ba da.
Kwamishinan wasanni na jihar Katsina Zakari Shargalle ya sanar da hakan a taron manema labarai a Katsina, a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban hukumar kwallon kafa ta kasa NFF Shariff Abdallah a lokacin da ya je Katsina don duba lamurran wannan sabuwar Kwalejin horar da kwallon kafa.
Zakari Shargalle ya ce kwallon kafa ta zamo sana’a mai kyau da duniya ke kallon akwai mafita a cikinta.
Ya ba da tabbacin cewa za a rika horar da ‘yan wasa yadda ya dace da kuma shiga a fita don sanya su murza leda a kulob-kulob din kasa har ma da na kasashen ketare hade da tallafin hukumar NFF.

APC ta zargi Kwankwaso da yiwa Ganduje zagon kasa gabanin zaben 2027

Kwankwaso 

APC ta zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Engr. Rabiu Kwankwaso da kitsa zagon kasa ga shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje, gabanin zaben 2027. 

Mai baiwa jam’iyyar APC shawara kan harkokin shari’a Farfesa Abdulkarim Kana ne ya yi wannan zargin yayin wata hira da gidan talabijin na Channels.

Abdulkarim yace shugabannin jam’iyyar NNPP na jihar Kano ke shirya zanga-zangar neman tsige Ganduje daga mukaminsa.

SERAP ta ba wa gwamnatin tarayya wa’adin sa’o’i 48 ta janye harajin CBN na 0.5%

Ƙungiyar kare hakkokin tattalin arziki ya yi gargadi ga Gwamnatin Tarayya da ta janye harajin kashi 0.5 cikin 100 da babban bankin Nijeriya CBN ya umurci bankunan ‘yan kasuwa da su rika cire wani kason kudi daga kwastominsu don samar da tsaro ga harkokin intanet.

SERAP ta kuma yi barazanar daukar matakin shari’a a kan gwamnati idan har bata janye harajin cikin wa’adin sa’o’i 48 da ta bada.

Kungiyar ta sanar da hakan ne a ranar Talata a shafinta na X, inda ta yi kira da a gaggauta janye lamarin.