Irin ukubar da ‘yan fanshon jihar Katsina ke sha kan layin tantance su cikin rana
Nijeriya za ta karfafa hadin gwiwa da sauran kasashe domin yaki da ta’addanci a Africa.
Nijeriya za ta karfafa hadin gwiwa da sauran kasashe domin yaki da ta’addanci a Africa.
Shugaba Bola Tinubu ya ce Nijeriya za ta ci gaba da karfafa hadin gwiwa da jagoranci wajen daukar matakan dakile ayyukan ta’addanci a Afirka.
Tinubu ya bayyana haka ne a wajen wani babban taron yaki da ta’addanci na kasashen Afirka da aka yi ranar Litinin a Abuja mai taken “Karfafa hadin gwiwar yanki da gina cibiyoyi don magance ci gaban barazanar ta’addanci a Afirka”.
Ya ce an inganta ayyukan yaki da ta’addanci a Nijeriya ta hanyar kafa dokar hana ta’addanci da kafa cibiyar yaki da ta’addanci ta Kasa, NCTC.
Shugaban ya ce, duk da haka dole ne nahiyar Afirka ta bi diddigin abubuwan da ke haifar da ta’addanci ta hanyar gudanar da shugabanci nagari, bin doka da oda, adalci da kuma hada kai.
Ya ce dole ne a baiwa ‘yan kasar tabbacin tsaron lafiyarsu ta hanyar tsare-tsare masu karfi da nufin kawar da matsalar ta’addanci.
Yaki da ta’addanci na bukatar cikakken tsari. Dole ne mu magance tushen abubuwan da ke haifar da tsatsauran ra’ayi, kamar talauci, warewar jama’a, da rashin adalci a cikin al’umma inji Tinubu
Mun kori biyu daga cikin dakarun mu dan tabbatar da mutunci da kwarewar aikin soja a Nijeriya -kakakin rundunar sojojin Nijeriya
Rundunar sojin Najeriya ta sanar da sallamar wasu daga cikin sojojin ta bayan samun su da laifi dumu-dumu na satar wasu wayoyin lantarki a matatar Dangote a daidai lokacin da ya kamata su kasance a bakin aiki.
Jam’in hulda da jama’a na rundunar sojojin, Manjo janar Onyema Nwachukwu ya tabbatar da korar sojojin biyu Kofur Innoson Joseph da Kofur Jacob Gani bayan gurfanar da su a kotun soji inda suka gagara musanta Laifuka da aka zarge su da aikatawa.
Ya ce an same su da laifin gaza gudanar da aikin su na soja kamar yadda dokar aikin soja sashe na 57 ya tanadar da kuma aikata wasu laifuka irin na farar hula ƙarƙashin tanadin kundin na 114 ƙaramin sashe na ɗaya a kundin dokokin aikin soja mai lamba A20 na shekarar 2004 a Najeriya.
Su dai korarrun sojojin biyu sun shiga hannu ne a sanadin wani mai suna Smart, wanda ya bukaci su raka shi ya ɗauki wadannan wayoyi da aka bari a kamfani, saidai da ya ga alamun zasu shiga hannu sai ya tsere ya bar su da jangwam.
Ƙirƙirar yan Sandan jihohi zai zama silar ƙãrin sãɓani a tsakanin ƙabilu-Sufeta janar na yan sandan Najeriya
Sufeta janar na yan sanda a Najeriya Olukayode Egbetokun ya ce Najeriya bata kai matsayin da zata yi ‘yan sandan jihohi ba saboda za’a riƙa samun umurni daga ɓangarori biyu wato bangaren gwamna da na sufeta janar.
Sufeta janar Olukayode yayi zargin akwai yiyuwar gwamnoni a Najeriya suyi amfani da yan sandan jihohi su wuce gona da iri da kuma take hakkokin yan Adam.
Olukayode Egbetokun ya baiyana cewa jihohi basu da wadãtar da zasu samar da irin ‘yan sandan da ƙasa ke bukata domin a kowace shekara ana buƙatar ɗaukar sãbin yan sanda dubu 30 kamar yadda majalisar ɗinkin Duniya ta bukaci a yi dan samar da ‘yan sanda na zamani.
Ya ce maimakon kirkiro yan sanda na jihohi, ƙãra gwamnati ta haɗe jami’an tsaro na civil defence dana hukumar kare haɗura ta ƙasa road safety wuri guda da yan sanda, ta yadda civil defence ɗin da jami’an roadsafty zasu zamo wasu sassan rundunar yan sanda.
Mu na so ka sake rage Naira 300 a farashin dizil a Najeriya
Bayan zabge Naira ɗari biyu da hamsin (250) a farashin ma’aunin lita guda na dizil, ƙungiyar dillalan man fetur a Najeriya IPMAN ta buƙaci matatar mai ta Dangote ta maida farashin litar ta dizil zuwa Naira ɗari bakwai (700).
Mataimakin shugaban kungiyar a Najeriya Hammed Fashola ya ce tunda yanzu babu maganar biyan kuɗin dakon man a jigin ruwa da kuma biya Kwatsam da sauransu, saboda a gida Najeriya ake haƙo tare da tãce man, akwai bukatar farashin ya sauƙa zuwa Naira 700.
Baya ga nuna farin cikin ƙungiyar ta IPMAN kan ragin Naira 250 da matatar Dangote ta yi a kuɗin na dizil, Mammed Fashola ya kuma ce la’akari da yadda darajar Naira ke ƙaruwa, babban dalili ne na rage kuɗin na dizil zuwa 700.
Matatar man ta Ɗangote dai ta fara rage kuɗin na dizil ne daga Naira 1,600 zuwa 1,250 makwanni biyu da suka gabata, sannan a mako da ya gabata kuma ta sanar da sake zabge Naira 250 a makon jiya.
Mutun sama da 4000 aka kashe da kuma garkuwa da su a farkon shekarar 2024.
An sake dakatar da Ganduje a APC daga mazabarsa, an ce ba ya biyan kudin harajin jam’iyya
Shugaban Nijeriya Bola ya amince da wasu tsare-tsare guda hudu don inganta fannin ilimi a kasar
Tsanar da ake yi wa ‘yan sanda na shafar tsaron Nijeriya in ji PCRC
Kishin arewa ya sa Shugaba Tinubu ya ba ‘yan yankin mukamai masu muhimmanci – Nuhu Ribadu



.jpg)
.jpg)
