Thursday, April 9, 2026
Home Blog Page 445

Farashin kayan abincin waje ya fi sauki fiye da na gida a Nijeriya

A yayin da Dala da CFA ke ci gaba da sauka a kasuwa, ana kara samun rahusa a kayakin abincin da ake shigo da su daga waje. Sai dai fa abincin da ake nomawa a kasar kuwa farashin bai sauka har yanzu.

Inda a wannan satin ake sayar da buhun masara N63,000 a kasuwar Mile 12 International Market da ke Lagos,a makonni biyu da suka shude ma haka ake saidawa a Kasuwar.
Ita kuwa Kasuwar Dawanau a jihar Kano kuɗin buhun masarar kara tashi ya yi duk da cewa tashin Dala da ake danganta tashi da tsadar kayan abinci ya sauka, inda a makon nan aka sai da buhun masara kan kudi N62,000, yayin da a makonnin baya aka sayar a N58,000.
A kasuwar Mai’adua jihar Katsina kuwa masarar ta ɗan sauka a makon nan, an dai sai da buhun kan kuɗi N60,000 a wannan makon na watan Shawwal, bayan da a watan Ramadan kuwa aka saida N62,000, an dai samu sauƙin N2,000 kenan kan farashin makonnin da suka wuce.
Hakazalika, masara ta sauka a kasuwar Kashere da ke Karamar Hukumar Akko a jihar Gombe, an sayi buhun masara N56-58,000 a satin nan, sai dai a sati biyu da suka gabata kuwa an sayar a kan kudi N60-65,000.
Ita ma dai kasuwar Giwa da ke jihar Kaduna Masarar ta fara sauka, an sayi buhun N57,000 a makon da ya gabata, amma a makon nan N55,000 ake sai da buhun.
To bari mu karkare farashin masara da kasuwar Gombi da ke jihar Adamawa, an sayar da buhun Masara N55-56-57,000 a satin nan, yayin da makonnin da suka shude aka sayar a kan kudi  N59-60,000 cif cif.
Shinkafar waje kuwa ta fi sauki a kasuwar Mai’adua jihar Katsina a wannan makon da ake sayar da buhun N58,000, yayin da a watan azumi aka sayar kan kudi N62,000, an dai samu ragowar N4000 kenan a ‘yan makonnin nan.
Shinkafar wajen ta fi tsada a kasuwar Zamani da ke jihar Adamawa da ake sayarwa N78,000 a wannan satin, yayin da a baya aka sayar kan kudi N80,000 daidai.
Ana saida buhun Shinkafar baturen N62,000 a wannan makon a kasuwar Dawanau da ke jihar Kano, amma makonnin da suka gabata an sayar da buhun kan kuɗi N66,000.
A kasuwar Mile 12 International Market dake Lagos kuɗin buhun Shinkafar Bature ya kama N75,000, haka nan aka saida a makonnin da suka shude ma.
Da DCL Hausa ta leka kasuwar Giwa da ke jihar Kaduna kuwa, N70,000 cif ake sai da buhun a makon nan da ke shirin karewa, yayin da a makonnin da suka gabata aka saida kan kudi  N78,000,an samu sauƙin N8000 kenan a wannan makon.
A kasuwar Kashere da ke jihar Gombe, an saida buhun Shinkafar Bature N82,000 a makonnin da suka wuce,sai dai a makon nan kuɗin buhun ya kama N75,000, an samu ragin N7000 kenan a makon nan dake dab da ƙarewa.
Ita ma dai shinkafar Hausa ta fi tsada a kasuwar Karamar hukumar Girie da ke jihar Adamawa, an sayar da buhun shinkafar Hausa N136,000 a makon nan, yayin da makon da ya gabata aka saida N140,000 an samu ragin N4000 akan farashin shinkafar na baya.
A kasuwar Mile 12 International Market da ke Lagos farashin buhun Shinkafa a wannan makon N130,000 ne, yayin da makon jiya aka sayar N120,000 cif.
Ita kuwa kasuwar Mai’adua jihar Katsina N110,000 ake sayar da buhun, bayan da makonnin da suka gabata aka sayar N120,000 an kara samun saukin N10,000 kenan a satin nan.
A kasuwar Giwa da ke jihar Kaduna kuwa, a makonnin da suka gabata ana sayar da buhun shinkafar N130,000 daidai, Haka nan batun bai sauya zani ba a makon nan .
Ita kuwa Kasuwar Kashere da ke jihar Gombe, an saida buhun Shinkafar ‘yar gida N135-140,000 a makonnin da suka shude, yayin da a makon nan aka sai da buhun N120-130,000.
Ana sai da buhun Shinkafar Hausa N110,000 a satin nan,yayinda makonnin da suka gabata ake saidawa 105,000, hakan na nuni da cewa an samu karin N5000 kenan a makon nan.
A bangaren Taliyar Spaghetti kuwa, ta fi tsada a kasuwar Mile 12 International Market da ke Lagos, inda ake saida kwalin N14,500, yayin da a makonnin da suka gabata ake sayarwa N13,500.
Ita ma dai kasuwar Dawanau da ke jihar Kano kuɗin Kwalin taliyar bai sauya zani ba,an sai da kwalin N13,500 a makonnin da suka shude,haka batun yake a makon nan dake dab da ƙarewa.
Idan muka yi tattaki zuwa Kasuwar Kashere da ke jihar Gombe kuwa, an saida kwalin taliyar N13,000 a wannan makon, yayin da makon da ya shude ake saidawa N13,300 a Kasuwar.
A kasuwar Mai’adua jihar Katsina ana sayar da taliyar N14,000 daidai a makonnin da suka gabata, sai dai a makon nan, N12,000 ake saidawa, an samu saukin 2000 kenan a wannan makon.
Yayin da a Kasuwar Giwa da ke jihar Kaduna kuwa ake saidawa N14,500, bayan da a makonnin da suka shude ake sayarwa N14,000 a samu karin N500 kenan a makon nan.
To a kasuwar zamani dake jihar Adamawa kuwa, An sai da kwalin taliya N13,200 a makonni biyu da suka gabata,yayinda a wannan makon ake Saidawa N13,000, daidai.
DCL HAUSA A’isha Usman Gebi

Atiku da Wike sun hadu, karon farko tun bayan zaben 2023, sai dai babu tabbacin ko sun gaisa

A karon farko tun bayan zaben 2023, Atiku Abubakar da Nyesom Wike sun hadu wajen guda don taron jam’iyyar PDP.

Sai dai Premium Times ta ce babu tabbacin ko sun gaisa a wajen taron.
Atiku Abubakar dai shi ne tsohon mataimakin shugaban kasar Nijeriya a zamanin mulkin Olusegun Obasanjo, yayin da Nyesom Wike ya yi Gwamnan jihar Rivers sau biyu, yanzu kuma shi ne ministan Abuja a gwamnatin APC.
Sauran wadanda suka halarci taron akwai tsohon mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo, shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa Abba Moro da Sanata Aminu Waziri Tambuwal, akwai tsohon Gwamnan jihar Kaduna kuma tsohon shugaban jam’iyyar ta PDP Ahmad Makarfi, da tsohon Gwamnan jihar Neja Babangida Aliyu, tsohon Gwamnan jihar Jigawa Sule Lamido da tsohon Gwamnan jihar Plateau Jonah Jang.

Fasinjoji sun yi sanadiyyar mutuwar wani jami’in kwastam a Katsina

Wasu bayanai da DCL Hausa ta tattara sun ce wasu fasinjoji da ke cikin wata babbar motar dakon kaya, sun yi sanadiyyar mutuwar wani jami’in kwastam a kan titin Katsina zuwa Dankama ta karamar Kaita a jihar.
Majiyar ta ce motar dakon kayan na dauke da mutane zuwa Dankama a lokacin da jami’an kwastam suka yi kokarin tsayar da ita, amma direban bai samu damar tsayawa ba. Hakan ne ya sa wani daga cikin jami’an kwastam din ya yi harbi da bindiga da aka yi zargin ya samu wani daga cikin fasinjojin da ke cikin motar a kugu.
Bayan da hakan ta faru ne direban babbar motar ya samu ya tsayar da motar, fasinjojin ciki suka sauko, suka durfafi jami’an na Kwastam da bayanai suka ce sun yi nasarar kama wanda ake zargi da yin harbin. 
Daga bisani bayanai suka ce, fasinjoji sun yi nasarar kashe jami’in kwastam din.
Sai dai daga bisani DCL Hausa ta samu labarin cewa shi ma wanda ake zargi jami’in na Kwastam ya harba a kugu mai suna Bashir Na-Buzuwa ya rasu.
Bashir mai kimanin shekaru 27 dan asalin garin Doro ta karamar hukumar Bindawa, na zaune ne a Unguwar Zanguna da ke cikin birnin Katsina.
Lamarin ya faru ne da misalin 10:27 na safiyar Larabar nan a daidai kauyen Gamjin Makaho da ke kan titin Katsina zuwa Dankama na karamar hukumar ta Kaita.
Amma jami’in hulda da jama’a na hukumar kwastam a jihar Katsina SC Tahir Balarabe a lokacin da DCL Hausa ta tuntube shi, ya ce za su fitar da sanarwa a hukumance, amma a lokacin ya ce su na kan kokarin yadda za su dauko gawar wanda ya rasa ran nasa.

Matsin tattalin arziki ya sa za a rufe kamfanonin sarrafa giya guda biyu a Nijeriya

 Matsin tattalin arziki ya sa za a rufe kamfanonin sarrafa giya guda biyu a Nijeriya

Kamfanin samar da giya na Nigerian Breweries na shirin rufe kamfanoni guda biyu,hakan nada nasaba ga ɗimbin matsalolin kuɗi da suke fuskanta, kamfanin ya bayyana hakan a ranar Talata a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Abubuwan da ke damun babban kamfanin sun hada da asarar musayar kudaden waje da aka yi a bara, wanda hakan ya sa ba shi da wani zabi illa rufe biyu daga cikin masana’antun.

Ya bayyana cewa wani babbar asarar da aka yi kan hada-hadar kudaden waje da ya kai Naira biliyan 153.3 ya sanya Kamfanin Breweries na Nijeriya ya yi babbar asara a bara, tun bayan da ya fara aiki shekaru 77 da suka gabata a kasar.

Asarar Naira biliyan 106.3 da aka yi a cikin 2023 ya samo asali ne daga matsalolin tattalin arziki da hauhawar farashin kayayyaki, rashin daidaituwar FX, da sauransu,kamar yadda kamfanin ya bayyana.

An sanar da kungiyoyin kwadagon da suka hada da kungiyar abinci da abin sha da ma’aikatar taba sigari da kuma kungiyar masu shayar da kayan sha da taba sigari kan matakin dakatar da aiki na wani dan lokaci a kamfanonin biyu, a cewar takardar.

Hukumar NDLEA ta lalata tare da kona kilogram 304,436 na muggan kwayoyi a Lagos

 Hukumar NDLEA ta lalata tare da kona kilogram 304,436 na muggan kwayoyi a Lagos.

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa, ta lalata jimillar kilogiram 304,436 da kuma lita 40,042 na haramtattun abubuwa da aka kama daga sassan jihohin Legas da Ogun a ranar talata.

Da yake jawabi a wajen wani bikin da aka lalata magungunan da aka kama a garin Badagry na jihar Legas, shugaban hukumar, Birgediya Janar Buba Marwa (mai ritaya) ya ce an lalata haramtattun kwayoyin da aka kama a fili biyo bayan umarnin da kotu bayar.

Daga nan sai ya yi kira da a kara tallafawa jama’a domin ci gaba da kokarin da hukumar NDLEA da sauran masu ruwa da tsaki ke yi na dakile illolin shaye-shayen miyagun kwayoyi da safarar miyagun kwayoyi a Nijeriya.

Marwa ya ce, “Duk da cewa ana gudanar da atisaye na yau da kullun da kuma tsari na kawar da abubuwa masu hadari daga cikin al’ummarmu, amma ana gudanar da lalatar da haramtattun kwayoyi a gaban jami’an kotu abubuwan da suka hada da haramtattun kwayoyi a jihohin da dama. haka kuma a ajujuwa daban-daban kamar su hodar iblis, da tabar heroin, da wiwi, da tramadol, da sauransu.

Ya ce jami’an hukumar ta NDLEA a sassa daban-daban na hukumar ne suka kama su a jihohin Legas da Ogun tun daga watan Janairun 2022 zuwa yau, musamman a tashoshin jiragen ruwa na Legas da filayen jiragen sama da kuma kan iyakokin kasa.

Matatar mai ta Dangote ta sanar rage farashin man dizal.

Matatar mai ta Dangote ta sanar rage farashin man dizal.
Makonni kadan da suka gabata, a lokacin da ta fara aiki, matatar mai ta Dangote ta sanya farashin man dizal a kan Naira 1,200.
Yayin da ake fitar da kayayyakin, matatar ta samar a kan farashi na Naira 1,200 ga kowace lita makonni uku da suka wuce.
Hakan ya nuna sama da kashi 30 cikin 100 na raguwar farashin kasuwa a baya na kusan Naira 1,600 kowace lita.
Sai dai a ranar Talata an kara samun raguwar Naira 200 a farashin, inda a yanzu farashin ya kai N1,000.
A ranar Larabar da ta gabata ne shugaban rukunin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya ce rage farashin man dizal zuwa Naira 1,200 zai yi tasiri ga hauhawar farashin kayayyaki a Nijeriya.
Ya yi wannan jawabi ne a wata ganawa da manema labarai bayan ziyarar da ya kai wa Shugaba Bola Tinubu na bikin Sallar a Legas.
A cewar Dangote, an samu ci gaban tattalin arziki a baya-bayan nan, wanda ke nuni da cewa kasar na kan turba mai kyau bisa matakan tattalin arziki da gwamnati ke dauka a halin yanzu.

Ana hasashen cewa ambaliyar ruwa za ta shafi jihohin Nijeriya 31 a bana

 Ana hasashen cewa ambaliyar ruwa za ta shafi jihohin Nijeriya 31 a bana

Gwamnatin tarayya ta rubutawa gwamnoni 31 takardar sanar da su halin da ake ciki na ambaliyar ruwa a jihohinsu tsakanin watan Afrilu zuwa Nuwamba na wannan shekara ta 2024.

Ministan albarkatun ruwa da tsaftar muhalli Farfesa Joseph Utsev ne ya bayyana hakan a ranar Talata a Abuja yayin da yake yi wa manema labarai karin haske kan hasashen ambaliyar ruwa na shekara ta 2024.

A wajen taron, hukumar kula da ayyukan ruwa ta Nijeriya, an bayyana cewa an ware kananan hukumomi 148 a jihohin Legas, Kano, Delta, da kuma wasu jihohi 28 a matsayin wuraren da ake fama da matsalar ambaliya.

Hasashen da aka samu na shekara ta 2024 na ambaliyar ruwa ya nuna cewa wani bangare na kananan hukumomi 148 a cikin jihohi 31 na tarayya sun fada cikin yankunan da ake fama da matsalar ambaliya, yayin da wani bangare na kananan hukumomi 249 da ke cikin jihohi 36 na tarayya da kuma babban birnin tarayya Abuja sun fada cikin tsaka mai wuya.

Jihohin da ke fama da matsalar ambaliya sun hada da Adamawa, Akwa-Ibom, Anambra, Bauchi, Bayelsa, Benue, Borno, Cross River, Delta, Ebonyi, Edo, Imo, Jigawa, Kaduna, Kano, Katsina, Kebbi, Kogi, Kwara, Legas , Nasarawa, Niger, Ogun, Ondo, Osun, Oyo, Plateau, Rivers, Sokoto, Taraba, Yobe.

Halartar taron Kwankwasiyya ya sa muka dakatar da gwamnan Kano daga jam’iyyarmu – NNPP

 

Tsagin jam’iyyar NNPP karkashin jagorancin Major Agbo ya sanar da dakatar da Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano daga cikin jam’iyyar.

A cikin sanarwar da Ogini Olaposi, sakataren jam’iyyar, ya fitar a yayin taron ‘yan jarida na wannan Talata a Abuja, tsagin jam’iyyar ta NNPP, ya ce rashin bayyana a gaban kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi shi ne ya sanya su daukar wannan mataki.  

Jaridar The Punch ta ce tsagin na NNPP ya fusata da halartar babban taron jam’iyyar da wani bangare karkashin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya jagoranta da gwamnan na Kano ya yi a ranar 06.04.2024. 

A jawabin Mr. Olaposi, ya ce ba su ga dalilin da gwamnan Kano zai halarci taron na Kwankwasiyya da a ganinsu haramtacce ne ba. Sai dai tuni wasu ‘yan Kwankwasiyya suka yi watsi da wannan dakatarwa daga jam’iyyar ta NNPP wacce a karkashinta ne aka zabi gwamnan na Kano da kuri’u sama da miliyan daya.

‘Yan bindiga sun kashe Sakataren jam’iyyar PDP a jihar Zamfara

 ‘Yan bindiga sun kashe Sakataren jam’iyyar PDP a jihar Zamfara 

‘Yan bindiga sun kashe Sakataren jam’iyyar PDP na karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.

Shugaban jam’iyyar PDP na karamar hukumar Garba Garewa ne ya tabbatar da kisan sakataren na jam’iyyar a Tsafe ga gidan talabijin na Channels ranar Talata.

 “Muna zargin wadanda suka kashe shi ‘yan fashi ne, sun shiga gidansa jiya (Litinin) suka harbe shi,” in ji Garewa.

Na hango za a kara shiga wahala a Nijeriya – Primate Ayodele

 Na hango za a kara shiga wahala a Nijeriya – Primate Ayodele 

Shugaban cocin INRI Evangelical Church, Primate Ayodele ya shawarci shugaban kasa Bola Tinubu da ya canza salonsa na farfado da tabarbarewar tattalin arziki saboda har yanzu akwai tarin matsalolin a fannin tattalin arziki a Nijeriya.

Ayodele ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Osho Oluwatosin ya sanya wa hannu.

Ya bayyana cewa har yanzu abubuwa za su ci gaba da tsada kuma za a kara samun hauhawar farashin kayayyaki matukar gwamnati ba ta inganta harkar noma da tabbatar da samar da man fetur mai sauki da kuma ci gaba da samar da wuraren da za rika tace man fetur a kasar.