‘Yan bindiga sun bude wa motar fasinja wuta a kauyen Katsina
Neman suna kungiyar NEF ke yi – Shugaba Tinubu na son arewa in ji minista Matawalle
Ganduje da matar sa zasu gurfana gaban kotu ranar 17 ga wannan wata na Aprilu
Wata babbar kotu a jihar Kano ta sanar da ranar 17 ga watan Afrilun wannan shekara a matsayin ranar da tsohon gwamnan Kano kuma shugaban jam’iyyar APC na ƙasa a yanzu, Abdullahi Ganduje da matar sa da wasu mutane shida za su gurfana a gaban ta bisa zargin su da aikata laifuka har kashi takwas da suka haɗa da na karkata wasu kuɗaɗen gwamnati da almundahana da ma batun karɓan cin hanci na dalolin Amurka da aka yi wa tsohon gwamnan Ganduje.
Kwamishinan Shari’a na jihar Kano Haruna Isa Dederi ya tabbatar da cewa an kammala hada dukkan takardu kan wannan Shari’a kuma za’a tura sammaci ga dukkan waɗanda ake zargi.
Kwamishinan Shari’a na Kanon ya ce abin da Ganduje bai fahimta ba shine bazai iya shã ba a wannan tuhume-tuhume, da yake fadin wai gwamnatin Kano bazata iya gurfanar da shi tare da kama shi da laifi ba saboda yana tãƙamar shi shugaban jam’iyyar APC ne na ƙasa, to amma ya sanī cewa wannan batu ne da ya shafi harkar jiha ba taraiya ba.
Yan kwanaki da suka wuce an jiwo Gwamna Abba Kabir Yusuf na Kano yana alwashin sai ya binciki Ganduje, saboda abin kunya da ya ce ya haifar wa jihar Kano.
Mahauci ya daɓa wa matar sa wuƙa a dalilin wayar salula
Gidauniyar MaiGemu Foundation ta yi wa marayu 3,000 dinkin sallah
GWAMNA NAMADI YA DAKATAR DA KWAMISHINAN KASUWANCI, AMINU KANTA.
GWAMNA NAMADI YA DAKATAR DA KWAMISHINAN KASUWANCI, AMINU KANTA.
Gwamnan Jihar Jigawa Malam Umar A Namadi, ya dakatar da kwamishinan kasuwancin jihar Alhaji Aminu Kanta har zuwa lokacin gudanar da bincike kan shirin ciyar war azumi a karamar hukumar Babura.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim.
Sanarwar ta ce matakin wani bangare ne na kudirin gwamnatin jihar na tabbatar da bin diddigin kudi da kuma tafiyar da kudaden gwamnati kamar yadda aka saba,wadda take nuni da cewa zai cigaba da zama harsai an kammala bincike
A cewar samarwar an dakatar da Kwamishinan ne bisa zarginsa da hannu wajen karkatar da asusun ciyar wa ta buda baki a da gwamnatin ta kaddamar a cikin azumi a karamar hukumar Babura,
‘Yan ta’adda sun bude wuta a kasuwar Yantumaki sun kashe mutane
Na ware N4.2m ga matasa masu amfani da soshiyal midiya su yi cefanen sallah – Engr Surajo Yazid Abukur
Farashin shinkafa ya fara karyewa a jihohi masu makwabtaka da Nijar
Shinkafar waje ta fara sauka a kasuwannin jihohin Kano da Katsina, inda a wannan makon aka saida buhun Shinkafar Baturen



