Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Al’umma na Nijeriya, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shimfiɗa tubali mai ƙarfi domin bunƙasar tattalin arziki na dogon lokaci da walwalar al’umma baki ɗaya.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi mambobin ƙungiyar Grassroots Advocacy for Tinubu (GAT) 2027 da suka kai masa ziyarar ban girma a Abuja, kamar yadda wata sanarwa daga Mataimaki na Musamman kan Harkokin Watsa Labarai, Malam Rabiu Ibrahim, ta nuna.
Alhaji Mohammed Idris ya ce gwamnatin Tinubu ta ɗauki matakai masu tsauri, wasu ma masu wahala, domin daidaita harkokin ƙasa da sanya Nijeriya kan hanya mai ɗorewa ta fuskar tattalin arziki.
Ya ƙara da cewa duk da ƙalubalen da ake fuskanta, alamu na fara bayyana na farfaɗowar tattalin arziki a muhimman fannoni, yana mai jaddada cewa manufofin gwamnatin na nufin samar da ci gaba mai dorewa da romon dimokuraɗiyya ga ’yan Nijeriya gaba ɗaya.
Kasashen Turai sun girke sojojin NATO a yankin Greenland sakamakon barazanar mamaye ta da Amurka ta yi
A cikin makon nan, kasashen Turai da dama sun fara tura sojoji zuwa Greenland a matsayin martani ga barazanar da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya maimaita na niyyar mallakar tsibirin ko da ta hanyar amfani da ƙarfi, lamarin da ya janyo rikicin siyasa da tsaro a yankin Arctic. 
Sojojin daga kasashen Denmark, Faransa, Jamus, Sweden, Norway, da Birtaniya sun isa Greenland domin wani aikin atisaye na haɗin gwiwa da ake kira Operation Arctic Endurance, wanda ƙasashen suka tsara domin ƙarfafa tsaron yankin da nuna goyon baya ga ikon Denmark a kan tsibirin. 
Kodayake yawan sojojin da aka tura ba shi da yawa, tura su yana da mahimmanci a matsayin sako ga duk wani yunkurin mamaye ko cin zarafin ‘yancin Greenland, wanda ke ƙarƙashin ikon Denmark kuma tushen tattaunawa cikin ƙungiyar NATO. 
Ma’aikatar tsaron Denmark ta ce manufar aikin atisayen ita ce inganta ƙarfin aiki a yanayin Arctic da kuma tabbatar da tsaro na haɗin gwiwa tare da abokan kawance. Hakanan an ba da sanarwar cewa za a iya ci gaba da matsawa da karfafa wannan rundunar tare da karin hadin kai daga ƙasashen kungiyar NATO a cikin shekarar 2026. 
An yi wa madugun adawar Uganda Bobi Wine daurin talala yayin da Shugaba Museveni ke kan gaba a zaben da ya gudana a kasar
Jami’an tsaro a Uganda sun tsare jagoran adawa Bobi Wine a gidansa, kwana guda bayan gudanar da zaɓen shugaban ƙasa, yayin da sakamakon farko ke nuna Shugaba Yoweri Museveni na kan gaba sosai.
Hukumar zaɓe ta Uganda ta ce bayan kidayar kusan kashi ɗaya cikin huɗu na ƙuri’u, Museveni ya samu kashi 76.25, yayin da Bobi Wine ya samu kashi 19.85, a zaɓen da ake sa ran za a fitar da sakamakonsa na ƙarshe da safiyar Asabar.
Jam’iyyar Bobi Wine, National Unity Platform, ta ce jami’an tsaro sun kewaye gidansa tare da hana shi fita, inda suka bayyana matakin a matsayin tsare shi a gida ba bisa ƙa’ida ba, yayin da ‘yan sanda da sojoji suka mamaye yankin.
Zaɓen dai ya gudana ne cikin matsin lamba, matsalolin injinan tantance masu zaɓe, da kuma katse intanet a faɗin ƙasar, lamarin da Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce ya nuna yanayi na tsangwama da tsoratarwa ga ‘yan adawa.
