Wednesday, April 8, 2026
Home Blog Page 45

Tinubu na shimfiɗa tubalin bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa — Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Al’umma na Nijeriya, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shimfiɗa tubali mai ƙarfi domin bunƙasar tattalin arziki na dogon lokaci da walwalar al’umma baki ɗaya.

Ministan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi mambobin ƙungiyar Grassroots Advocacy for Tinubu (GAT) 2027 da suka kai masa ziyarar ban girma a Abuja, kamar yadda wata sanarwa daga Mataimaki na Musamman kan Harkokin Watsa Labarai, Malam Rabiu Ibrahim, ta nuna.

Alhaji Mohammed Idris ya ce gwamnatin Tinubu ta ɗauki matakai masu tsauri, wasu ma masu wahala, domin daidaita harkokin ƙasa da sanya Nijeriya kan hanya mai ɗorewa ta fuskar tattalin arziki.

Ya ƙara da cewa duk da ƙalubalen da ake fuskanta, alamu na fara bayyana na farfaɗowar tattalin arziki a muhimman fannoni, yana mai jaddada cewa manufofin gwamnatin na nufin samar da ci gaba mai dorewa da romon dimokuraɗiyya ga ’yan Nijeriya gaba ɗaya.

Gwamnan Jihar Plateau, Muftwang ya yi ta’aziyyar Limamin da ya tseratar da Kiristoci 262 a jihar

0

A cikin makon nan, kasashen Turai da dama sun fara tura sojoji zuwa Greenland a matsayin martani ga barazanar da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya maimaita na niyyar mallakar tsibirin ko da ta hanyar amfani da ƙarfi, lamarin da ya janyo rikicin siyasa da tsaro a yankin Arctic. 

Sojojin daga kasashen Denmark, Faransa, Jamus, Sweden, Norway, da Birtaniya sun isa Greenland domin wani aikin atisaye na haɗin gwiwa da ake kira Operation Arctic Endurance, wanda ƙasashen suka tsara domin ƙarfafa tsaron yankin da nuna goyon baya ga ikon Denmark a kan tsibirin. 

Kodayake yawan sojojin da aka tura ba shi da yawa, tura su yana da mahimmanci a matsayin sako ga duk wani yunkurin mamaye ko cin zarafin ‘yancin Greenland, wanda ke ƙarƙashin ikon Denmark kuma tushen tattaunawa cikin ƙungiyar NATO. 

Ma’aikatar tsaron Denmark ta ce manufar aikin atisayen ita ce inganta ƙarfin aiki a yanayin Arctic da kuma tabbatar da tsaro na haɗin gwiwa tare da abokan kawance. Hakanan an ba da sanarwar cewa za a iya ci gaba da matsawa da karfafa wannan rundunar tare da karin hadin kai daga ƙasashen kungiyar NATO a cikin shekarar 2026. 

Kasashen Turai sun girke sojojin NATO a yankin Greenland sakamakon barazanar mamaye ta da Amurka ta yi

0

A cikin makon nan, kasashen Turai da dama sun fara tura sojoji zuwa Greenland a matsayin martani ga barazanar da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya maimaita na niyyar mallakar tsibirin ko da ta hanyar amfani da ƙarfi, lamarin da ya janyo rikicin siyasa da tsaro a yankin Arctic. 

Sojojin daga kasashen Denmark, Faransa, Jamus, Sweden, Norway, da Birtaniya sun isa Greenland domin wani aikin atisaye na haɗin gwiwa da ake kira Operation Arctic Endurance, wanda ƙasashen suka tsara domin ƙarfafa tsaron yankin da nuna goyon baya ga ikon Denmark a kan tsibirin. 

Kodayake yawan sojojin da aka tura ba shi da yawa, tura su yana da mahimmanci a matsayin sako ga duk wani yunkurin mamaye ko cin zarafin ‘yancin Greenland, wanda ke ƙarƙashin ikon Denmark kuma tushen tattaunawa cikin ƙungiyar NATO. 

Ma’aikatar tsaron Denmark ta ce manufar aikin atisayen ita ce inganta ƙarfin aiki a yanayin Arctic da kuma tabbatar da tsaro na haɗin gwiwa tare da abokan kawance. Hakanan an ba da sanarwar cewa za a iya ci gaba da matsawa da karfafa wannan rundunar tare da karin hadin kai daga ƙasashen kungiyar NATO a cikin shekarar 2026. 

An yi wa madugun adawar Uganda Bobi Wine daurin talala yayin da Shugaba Museveni ke kan gaba a zaben da ya gudana a kasar

0

Jami’an tsaro a Uganda sun tsare jagoran adawa Bobi Wine a gidansa, kwana guda bayan gudanar da zaɓen shugaban ƙasa, yayin da sakamakon farko ke nuna Shugaba Yoweri Museveni na kan gaba sosai.

Hukumar zaɓe ta Uganda ta ce bayan kidayar kusan kashi ɗaya cikin huɗu na ƙuri’u, Museveni ya samu kashi 76.25, yayin da Bobi Wine ya samu kashi 19.85, a zaɓen da ake sa ran za a fitar da sakamakonsa na ƙarshe da safiyar Asabar.

Jam’iyyar Bobi Wine, National Unity Platform, ta ce jami’an tsaro sun kewaye gidansa tare da hana shi fita, inda suka bayyana matakin a matsayin tsare shi a gida ba bisa ƙa’ida ba, yayin da ‘yan sanda da sojoji suka mamaye yankin.

Zaɓen dai ya gudana ne cikin matsin lamba, matsalolin injinan tantance masu zaɓe, da kuma katse intanet a faɗin ƙasar, lamarin da Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce ya nuna yanayi na tsangwama da tsoratarwa ga ‘yan adawa.

‘Yan sanda sun kama magidancin da ake zargin ya yi ajalin matarsa da fartanya a jihar Kebbi

0

Rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi ta kama wani mutum mai shekara 30, Suleman Mamuda, bisa zargin halaka matarsa Umaima Maidawa a unguwar Bayawa da ke Karamar Hukumar Augie ta jihar.

Mai magana da yawun rundunar, SP Bashir Usman, ya ce ana zargin Mamuda da dukan matarsa da sandar iccen fartanya, lamarin da ya yi sanadin ajalinta.

Ya bayyana cewa bayan faruwar lamarin, wanda ake zargin ya tsere daga yankin, amma daga bisani jami’an tsaro suka gano inda yake tare da cafke shi sakamakon bincike da bayanan sirri daga al’ummar yankin.

Rundunar ta ce Kwamishinan ’Yan Sanda, CP Umar Mohammed Hadejia, ya bayar da umarnin mika shi zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) domin ci gaba da bincike da gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu.

Kashim Shettima ya bar Abuja domin wakiltar Tinubu wajen bikin rantsar da Shugaban Guinea-Conakry, Mamadi Doumbouya

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya tashi daga Abuja domin wakiltar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar Guinea-Conakry, Mamadi Doumbouya. Bayan wannan, zai halarci taron shekara-shekara na World Economic Forum (WEF 2026) a Davos, Switzerland, daga 19 zuwa 23 ga Janairu.

Shugaba Doumbouya zai karbi rantsuwa a GLC Stadium, Nongo, a ranar Asabar, 17 ga Janairu. Halartar Shettima yana da nufin ƙarfafa jagorancin Najeriya a ECOWAS, tallafawa dawowar Guinea ga tsarin mulki, da kuma zurfafa hulɗar tattalin arziki tsakanin ƙasashen biyu.

A baya-bayan nan, fitar da kayayyakin Najeriya zuwa Guinea, musamman kayan masana’antu da noma, ya kai dala miliyan 3.29.

Bayan Guinea, Mataimakin Shugaban Nijeriya zai shiga WEF 2026 a Davos, inda shugabanni daga gwamnatoci, kasuwanni, ƙungiyoyi, da masana kimiyya za su tattauna kan ci gaban fasahar zamani kamar AI, quantum computing, biotechnology, da makamantansu. Taron zai mayar da hankali ne kan yadda za a yi amfani da waɗannan fasahohi don haɓaka tattalin arziki, samar da damar aiki, da ci gaba mai ɗorewa.

Shettima zai yi amfani da damar wajen tattaunawa da shugabanni da masu zuba jari kan tsare-tsaren gyaran tattalin arziki na Nijeriya, damar zuba jari, da rawar da Afirka ke takawa wajen ƙirƙirar makoma mai ɗorewa. Ana sa ran zai dawo Najeriya bayan kammala ayyukansa a Davos.

Gwamnatin Nijeriya ta gargadi jihohi kan yin sulhu da ‘yan bindigar daji

Gwamnatin Nijeriya ta gargadi gwamnatocin jihohi da kada su shiga yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, tana mai cewa irin wannan sulhu yaudara ce kuma na kara tabarbarewar tsaro.

Ministan Tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa (ritaya), ya bayyana haka a wata hira da BBC Hausa inda ya ce an taba gargadin Jihar Katsina kan irin wadannan shirye-shiryen, yana mai jan hankalin al’umma da su daina duk wata mu’amala da ’yan bindiga, ciki har da sayar musu da abinci ko kayan bukata.

Ya ce hadin kan jama’a da bayar da sahihin bayanan sirri na da matukar muhimmanci wajen dakile ’yan bindiga kuma duk wanda ya sayar musu da abinci yana cin kudin jini ne.

Ministan ya kuma musanta rade-radin cewa Gwamnatin Nijeriya na biyan kudin fansa, yana mai cewa sojoji na amfani da matsin lamba da bayanan sirri ne wajen ceto wadanda aka sace.

A cewarsa, biyan kudin fansa na kara karfafa aikata laifuka, tare da kira ga iyalai da al’umma su rika kai rahoton sace-sace ga hukumomin tsaro maimakon shiga tattaunawa da masu garkuwa.

Limamin da ya ceci Kiristoci 262 lokacin rikicin addini a jihar Plateau ya rasu

0

Limamin garin Nghar da ke Karamar Hukumar Barkin Ladi a Jihar Plateau, Abubakar Abdullahi, wanda ya shahara da ceton Kiristoci 262 a rikicin addini na 2018, ya rasu yana da shekara 90.

Ɗansa, Saleh Abubakar, ya tabbatar wa Daily Trust cewa mahaifinsa ya rasu ne a daren Alhamis a Asibitin Kwararru na Plateau da ke Jos, bayan kwana goma da kwantar da shi sakamakon ciwon zuciya da ya dade yana fama da shi.

Marigayin ya bar ’ya’ya 19, maza 12 da mata bakwai. Za a yi jana’izarsa ne a yau Juma’a bayan sallar Juma’a a garin Nghar.

A watan Yunin 2018, yayin rikicin addini da ya shafi kauyuka 10 a Barkin Ladi, Limamin ya boye Kiristoci 262 a masallaci da gidansa har rikicin ya lafa, lamarin da ya ceci rayukansu. Saboda wannan jarumta, ya samu lambobin yabo da dama, ciki har da International Religious Freedom Award daga Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka a 2019.

Dokokin harajin Tinubu za su kare martabar masu karamin karfi a Nijeriya – Taiwo Oyedele

0

Shugaban Kwamitin Shugaban Kasa kan Gyaran Tsarin Haraji, Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa kananan masu zuba jari a kasuwar hannayen jari ba su da alhakin biyan harajin ribar jari, yana mai cewa dokar haraji ta 2026 ta fi mayar da hankali ne kan kare masu karamin karfi da kara kudin hannun jama’a.

Oyedele ya fadi haka ne a taron Cowry Quarterly Economic Discourse, inda ya ce dokar ta ba da cikakken rangwame ga duk wanda kudin da ya samu daga sayar da kadarori bai wuce Naira miliyan 150 ba, kuma ribar ba ta haura Naira miliyan 10 cikin watanni 12, ba tare da wani sharadi ba.

Ya kara da cewa manyan masu kudi ne kawai ke biyan harajin idan sun fice daga zuba jari gaba daya ba tare da sake zuba kudin ba, yayin da kudin da aka sake zubawa ke samun rangwame. Ya ce wannan tsarin yana karfafa ci gaban kasuwar jari da bunkasar tattalin arziki.

Oyedele ya kuma bayyana cewa dokar haraji ta 2026 ta kawo karshen “harajin talauci,” inda ya ce ma’aikatan da ke karbar mafi karancin albashi ba sa biyan harajin shiga kwata-kwata, tare da kara ka’idar cewa masu karfin biyan haraji su fi daukar nauyi.

Amurka za ta kashe $413m kan yaƙi da matsalar tsaro a Nijeriya da Afirka a 2026

Gwamnatin Amurka ta ware kusan Naira biliyan 587 domin ayyukan yaki da ta’addanci a Nijeriya da wasu kasashen Afirka a shekarar 2026, sakamakon tabarbarewar tsaro a yankin Yammacin Afirka.

Kudaden suna cikin Dokar Kasafin Tsaron Amurka ta 2026 (NDAA), wadda ta amince da kashe dala miliyan 413.046 ga rundunar sojin Amurka a Afrika (AFRICOM), kamar yadda takardun da aka samu suka nuna. Dokar ta samu sahalewar Shugaban Amurka, Donald Trump, a ranar 18 ga Disamba, 2025.

Kasafin ya zo ne a lokacin da Nijeriya ke fama da ta’addanci a Arewa maso Gabas, fashin daji a Arewa maso Yamma, da kuma laifukan teku a Tekun Guinea, yayin da kasashen Mali da Benin ke fama da hare-haren ‘yan jihadi daga yankin Sahel.

Dokar ta kuma tanadi kafa ofishin Mataimakin Sakataren Harkokin Afirka a Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, domin sa ido da daidaita manufofin Amurka a Afirka ta Kudu da Sahara, tare da bibiyar tasirin dabarun soja na Rasha a nahiyar.